Tarbiyya A Wajen Malaman Shi’a, Musamman A Mahangar Falsafar Tarbiyya Da Akhlāq A Fikirar Ahlul Bayt (a.s). Tarbiyya tana nufin tsari na ilmantarwa da gina ɗan adam don isa zuwa ga kamala (Samun yardan Allah ) – wato kai mutum zuwa matakin da Allah Yake so, ta hanyar gyara Aƙida, ladubba, da halaye, da kuma shiryar da zuciya zuwa ga Ubangiji (Mahalicci). 🔹 Ma’anar “Tarbiyya” A Harshen Shi’a: Kalmar "Tarbiyya" tana nufin: "Nuna kulawa da gina mutum daga matakin ƙanƙanta zuwa manyanta, tare da ci gaba da tsare shi a kowane mataki na ci gaba – har ya kai ga kamala (Samun yardan Allah). Saboda haka, tarbiyya a mahangar Shi'a ba kawai koyar da ilimi ba ce, amma gyaran ruhi ne, halayya, da tunani, bisa koyarwar Qur’ani da Ahlul Bayt (a.s). Mahimmancin Tarbiyya A Makarantar Ahlul Bayt (a.s): 1. Tarbiyyar Imani: Tarbiyyantar da mutum a kan gaskata da kaɗaita Allah (tawhīd), Ma’ad (Makoma ƙiyama), Annabta, da Imama. Wannan shi ne tushen tarbiyya. 2. Tarbiyyar Akhlaqi (Halaye...
Ta Yaya Albarka Ke Ƙaruwa A Gida? Amirul Muminin Ali (a.s) ya ce: (Gidan da ake karanta Alqur'ani a cikinsa, kuma ake ambaton Allah Ta'ala, albarkarSa tana yawaita, Mala'iku suna halartarsa (cikin gidan), shaidanu suna barinsa, kuma (gidan) yana haskakawa ga mazauna sammai kamar yadda taurari ke haskakawa ga mutanen ƙasa, amma gidan da ba a karanta Alkur'ani a cikinsa, kuma ba a ambaton Allah, albarkarsa tana raguwa, kuma mala'iku suna barinsa, shaiɗani suna halartan gidan. Masdar: Al-Kafi, juzu'i na 2, shafi na 499. 27/05/2024, Emran Darussalam