Skip to main content

Posts

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...
Recent posts

Daga Kyawawan Dabi'un Imam Aliyu Zainul Abidin (AS)

Daga Kyawawan Dabi'un Imam Aliyu Zainul Abidin (AS) Imam Zainul Abidin (A.S.) ya kasance yana sa ido da kula kan ayarin mahajjata da ke zuwa daga wurare masu nisa suna ratsa birnin Madina.  Wata rana ya shiga cikin ɗaya daga cikin ayarin da suka taho, yana mai ce musu yana so ya yi aiki a matsayin bawa mai yi wa mahajjata hidima. A wancan lokaci ana yin tafiya ne a kan dawakai da rakuma, kuma tafiyar tana ɗaukar kwanaki goma ko fiye. A duk wannan lokaci, Imam (A.S.) yana mai da hankali sosai wajen yi wa mahajjata da matafiya hidima, da biya musu bukatu da bin umarninsu. Wata rana a hanya sai ayarin da Imam yake tare da su suka haɗu da wani da ya san shi. Mutumin ya yi matuƙar mamaki da abin da ya gani, Imami yana hidima wa ayarin mahajjata, sai ya tambayi mutanen ayarin cewa: “Wane ne wannan da kuka taho tare da shi yana yi muku hidima a hanya?” Sai suka ce: “Hakika ba mu san shi ba; wani kyakkyawan saurayi ne muka haɗu da shi a Madina, ya ba mu kansa don ya yi mana hidima, sai muk...

Sirrin Barin Aikata Saɓo

Ayatullah Muhammad Taƙi Bahjah Yace: Da, da rana mun kasance muna shagaltuwa da mayar da hankali ga Allah da bauta masa, da mun sami dacewar tashi yin sallar tahajjud da asuba. “Dacewar yin sallar dare na iya kasancewa a cikin barin saɓawa Allah” Emran Darussalam 

Mafi Daɗin Zance

A cikin Tafsirin Al-Mīzān na Allāma Ṭabāṭabā’ī, abin da ake nufi da faɗin Allah Madaukaki: إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ shi ne: “zuciyar da babu wata alaƙa a cikinta da wani abu face Allah kaɗai.” Ƙarin bayani kan maganar Allāma kuwa shi ne: "ba ma’anarta shine wannan zuciya ba ta son wani sai Allah kaɗai ba, domin babu laifi son wanin Allah. Amma abin da ake nufi shi ne zuciyar ta kasance tana da mafi ƙarfin alaƙa da ƙauna ga Allah fiye da komai da kowa, kamar yadda Allah Madaukaki Ya ce: وَالَّذِينَ آمَنُوا أَشَدُّ حُبًّا لِلَّهِ “Waɗanda suka yi imani su ne mafi tsananin soyayya ga Allah.” 21/01/2025, Emran Darussalam.

Aikin Rana

Aikin rana shi ne haskakawa ko da tana bayan gajimare ne, haka ma Hujja (Atfs) aikin shi shine shiryarwa ko da yana boyayye ne gare mu a cikin hijabin ɓoyuwa (Gaiba), kamar yadda Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa) ya ce. Idanunmu ba sa iya ganinsa, amma akwai wani rukuni na jama'a da suka rika ganinsa kuma har yanzu suna ganinsa; kuma ko da ba sa ganinsa (a yanzu) to suna da alaƙa da shi. Touch and hold a clip to pin it. Unpinned clips will be deleted after 1 hour.Touch and hold a clip to pin it. Unpinned clips will be deleted after 1 hour.Touch and hold a clip to pin it. Unpinned clips will be deleted after 1 hour.Touch and hold a clip to pin it. Unpinned clips will be deleted after 1 hour.Use the edit icon to pin, add or delete clips.Touch and hold a clip to pin it. Unpinned clips will be deleted after 1 hour.Touch and hold a clip to pin it. Unpinned clips will be deleted after 1 hour.Use the edit icon to pin, add or delete clips.Touch and hol...

🌙 Falalar Azumin Watan Sha‘abān daga Ahlul Baiti (A.S).

🌙 Falalar Azumin Watan Sha‘abān daga Ahlul Baiti (A.S). Sha‘abān watan Annabi (S). Imam Ali (A.S) ya ruwaito cewa Manzon Allah (S) ya ce: “Sha‘abān watana ne, wanda ya yi azumi rana ɗaya a cikinsa, Aljanna ta wajaba a gare shi.” 📚 Duba littafin " Wasā’ilu sh-Shī‘a" Azumi a Sha‘abān yana jawo gafarar zunubai. Imam Ja‘afar As-Sadiq (A.S) ya ce: “Duk wanda ya yi azumi a kwanaki uku na ƙarshen watan Sha‘abān, Allah zai rubuta masa azumin wata biyu a jere.” 📚 Duba littafin " Bihārul Anwār" Sha‘abān shiri ne ga Ramadān. Imam Ali (A.S) ya ce: “Manzon Allah (S) yana yawaita azumi a watan Sha‘abān, yana haɗa shi da Ramadān.” 📚 Duba littafin " Nahjul Balāgha " (ma’ana daga ruwayoyi). Azumin Sha‘abān yana horar da rai, yana tsaftace zuciya, kuma yana shirya bawa ga Ramadān. Azumin Sha‘abān kariya ce daga wuta . Imam Ar-Ridha (A.S) ya ce: “Duk wanda ya yi azumi a Sha‘abān saboda ƙaunar Annabi (S), Allah zai ƙaunace shi, Ya kuma kare shi daga wutar Jahannama.” 📚 D...

Ummoul Masa'ib Zainaba (AS)

Dukkanin cikar kamala da darajoji da aka samu a wajen wanzuwar darajar Manzon Allah ﷺ da iyalansa, Sayyida Khadijah da Siddiqah Al-Kubra Fatimah Az-Zahra, da Amirul Mumineen (tsira da amincin Allah su tabbata a gare su gaba ɗaya), duka akwai su kuma sun bayyana a wanzuwar darajar Sayyida Zainab (tsira da amincin Allah su tabbata a gare ta). Manzon Allah ﷺ da iyalansa sun ce duk wanda ya yi kuka a kan wannan jaruma, to kamar ya yi kuka ne a kan 'yan uwanta biyu, Imam Hasan da Husain (tsira da amincin Allah su tabbata a gare su). Ma'ana, hawaye guda daya a kan juyayin Sayyida Zainab yana daidai ne da kuka a kan juyayin Imamai biyu ma'asumai (tsira da amincin Allah su tabbata a gare su gaba ɗaya). 15 Ga Watan Rajab Shahadan Sayyida Zainab, Ya Allah Ka Ƙara Mana Ƙaunarta. Sayyid Ahmad Al-Musawi. Fassara: Emran Darussalam.