Ta Yaya Albarka Ke Ƙaruwa A Gida? Amirul Muminin Ali (a.s) ya ce: (Gidan da ake karanta Alqur'ani a cikinsa, kuma ake ambaton Allah Ta'ala, albarkarSa tana yawaita, Mala'iku suna halartarsa (cikin gidan), shaidanu suna barinsa, kuma (gidan) yana haskakawa ga mazauna sammai kamar yadda taurari ke haskakawa ga mutanen ƙasa, amma gidan da ba a karanta Alkur'ani a cikinsa, kuma ba a ambaton Allah, albarkarsa tana raguwa, kuma mala'iku suna barinsa, shaiɗani suna halartan gidan. Masdar: Al-Kafi, juzu'i na 2, shafi na 499. 27/05/2024, Emran Darussalam
Kwaɗaitarwa Kan Azumin Ranar Arfa da Ayyukan Cikinta Ranar Arfa tana daga cikin mafi girman ranaku a Musulunci, rana ce ta rahama, gafara, karɓar addu’a da kusanci ga Allah Maɗaukaki. Ita ce ranar tara ga watan Zul-Hijja, ranar da mahajjata suke tsayuwa a filin Arfa suna roƙon Ubangijinsu cikin tawali’u da kuka. An rawaito daga Manzon Allah (S.A.W) cewa azumin ranar Arfa yana kankare zunuban shekara biyu; shekarar da ta gabata da kuma mai zuwa. Wannan wata babbar dama ce ga masu neman gafarar Allah da tsarkake zukata. Falalar Azumin Ranar Arfa Azumin ranar Arfa na daga cikin ibadun da malamai suka yi matuƙar kwaɗaitarwa a kansa ga waɗanda ba sa aikin Hajji. Rana ce da: Allah ke yawaita ‘yanta bayinsa daga wuta. Addu’o’i suke samun karɓuwa. Rahama da albarka suke sauka. Zuciya take samun nutsuwa da kusanci ga Allah. Saboda haka kada mu bari wannan rana ta wuce ba tare da: azumi, addu’a, istigfari, salati ga Annabi da Ahlulbaitinsa (A.S), karatun Alƙur’ani, da yawaita ambaton Allah ba. M...