Daren Nisfu Sha’aban
Mai girma da ɗaukaka yana cewa:
(Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133.
Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.”
Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.”
Kuma an rawaito daga al-Baqir (A.S) cewa: “Shi ne mafi falalar dare bayan Daren lailatul Qadari; a cikinsa Allah Madaukaki yana bai wa bayinSa falalarSa, kuma Yana gafarta musu da ni’imarSa. Don haka ku yi ƙoƙari wajen kusantar Allah a cikinsa, domin dare ne da Allah ya yiwa Kansa alƙawari cewa ba Zai mayar da roƙon mai roƙo a cikinsa ba, matuƙar bai roƙi saɓo ba. Kuma shi ne daren da Allah ya tanadar mana (mu) Ahlul Baiti daidai da yadda Ya tanadar da daren lailatul Qadri ga Annabinmu (S). Don haka ku yi ƙoƙari wajen addu’a da tsarkake Allah a cikinsa”
Daren nisfu Sha’aban yana daga cikin manyan darare masu girma a cikin shekara. Saboda haka ya dace mumini ya kula da shi, ya raya shi da muhimmanci; domin raya sunnah da bin umarnin Imamai (A.S) ga mabiyansu na yin ƙoƙari a ibada, da kuma cin moriyar wannan dama mai girma da ke tattare da kyaututtukan Allah a wannan dare.
Dare ne na karɓar addu’a, gafarar zunubai, da ‘yantar da wuyoyi daga wuta.
Ya Allah Ka Bada Iko, Kada Ku Manta Damu Cikin Addu'oinku.
Tue, Feb 3,
2026.
Comments
Post a Comment