Skip to main content

Juma’ar Ƙarshe A Watan Sha’aban.

Juma’ar Ƙarshe A Watan Sha’aban.

Watan Sha’aban wata ne mai girma a riwayoyin Ahlulbaiti (A.S) da wasunsu, – musamman Juma’ar ƙarshe – tana da muhimmanci saboda tana zama tamkar gada tsakanin Sha’aban da Ramadan.

An rawaito daga Annabi Muhammad (S) cewa:
“Sha’aban wata na ne, kuma Ramadan watan Allah ne.”
(Bihar al-Anwar na Allama al-Majlisi)

Wannan yana nuna cewa Sha’aban wata ne na salati da kusanci da Annabi (S.A.W), kuma Juma’ar ƙarshe a cikinsa tana zama dama na shiri ga Ramadan.

Dalilin Muhimmancin Juma’ar Ƙarshe a Sha’aban:
- Kammala Sha’aban da Tuba – Domin a shiga Ramadan cikin tsarki.
- Yawaita Salati – Saboda Sha’aban wata ne na Annabi.
- Neman gafara kafin watan rahama.

An rawaito daga Imam Ali ibn Abi Talib (A.S) cewa:
“Ku yawaita istigfari da salati a Sha’aban.”

Ayyukan Juma’ar Ƙarshe a Sha’aban

1. Yin Ghusl na Juma’a (wanka)
Ghusl mustahabbi ne mai ƙarfi.
Imam Sadiq (A.S) ya ce:
“Wankan Juma’a tsarkakewa ne daga zunubai har zuwa Juma’a ta gaba.”
( Al-Kafi na Muhammad ibn Ya'qub al-Kulayni)

2. Yawaita Salati ga Annabi da Ahlulbait (A.S)
A Sha’aban an fi ƙarfafa salati.
An rawaito daga Imam Ja'far al-Sadiq (A.S):
“Wanda ya yi salati ga Muhammad da Ahlulbaitinsa a Sha’aban, Allah zai saukar masa da rahama.”

3. Karatun Munajatin Sha’aban
Daya daga cikin muhimman ayyuka shi ne Munajatin Sha’aban, wadda aka rawaito daga Imam Ali ibn Abi Talib da sauran Imamai.
An kawo shi a cikin Mafatih al-Jinan na Shaykh Abbas al-Qummi.

4. Azumi (Idan Bai Zo Ramadan Ba).
Idan Juma’ar ƙarshe ba ta yi daidai da ranar shakku ba (ranar 30 Sha’aban da ake tantama ko shakka), ana iya yin azumi mustahabbi.
An rawaito daga Imam Muhammad al-Baqir (A.S):
“Azumin Sha’aban kariya ne daga wuta.”

5. Istigfari Mai Yawa
Ana son a karanta:
“Astaghfirullaha wa as’aluhut-tawbah”
Sau 70 ko fiye.

6. Niyya da Shiri Ga Ramadan
A riwayoyi an nuna cewa mutum ya:
Biya bashin ibada
Gyara hulɗa da mutane
Nemi gafara
Domin shiga Ramadan cikin tsarki.

Hikimar Juma’ar Ƙarshe a Sha’aban:
- Dama ta ƙarshe ta shiri kafin watan saukar Alƙur’ani.
- Wanke zuciya da salati.
- Kammala Sha’aban da kyakkyawan ƙarshe.

Kammalawa
A fahimtar Ahlulbaiti (A.S), Juma’ar ƙarshe a Sha’aban wata babbar dama ce ta:
Tuba
Salati
Munajati
Shiri ga Ramadan

Ya Allah Ka Sanyamu Cikin Waɗanda Kake Goge Zunubansu Da Ƴantasu Daga Wuta Zuwa Aljanna.

Fri, Feb 13
2026.
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...