Daga Kyawawan Dabi'un Imam Aliyu Zainul Abidin (AS)
Imam Zainul Abidin (A.S.) ya kasance yana sa ido da kula kan ayarin mahajjata da ke zuwa daga wurare masu nisa suna ratsa birnin Madina.
Wata rana ya shiga cikin ɗaya daga cikin ayarin da suka taho, yana mai ce musu yana so ya yi aiki a matsayin bawa mai yi wa mahajjata hidima. A wancan lokaci ana yin tafiya ne a kan dawakai da rakuma, kuma tafiyar tana ɗaukar kwanaki goma ko fiye. A duk wannan lokaci, Imam (A.S.) yana mai da hankali sosai wajen yi wa mahajjata da matafiya hidima, da biya musu bukatu da bin umarninsu.
Wata rana a hanya sai ayarin da Imam yake tare da su suka haɗu da wani da ya san shi. Mutumin ya yi matuƙar mamaki da abin da ya gani, Imami yana hidima wa ayarin mahajjata, sai ya tambayi mutanen ayarin cewa: “Wane ne wannan da kuka taho tare da shi yana yi muku hidima a hanya?”
Sai suka ce: “Hakika ba mu san shi ba; wani kyakkyawan saurayi ne muka haɗu da shi a Madina, ya ba mu kansa don ya yi mana hidima, sai muka yarda muka taho da shi.”
Nan mutumin ya ce: “Da kun san ko wanene shi, da ba ku ɗauke shi a matsayin bawa kuna ba shi umarni da hani ba… domin kuwa shi ne Ali ɗan Husaini ɗan Ali ɗan Abi Talib (A.S.)! Shi ne ɗan Manzon Allah (S)”
A nan ne mutanen ayarin suka garzaya zuwa ga Imam Zainul Abidin (A.S.), suka rusuna suna sumbatar hannuwansa da ƙafafunsa, suna cewa: “Ya ɗan Manzon Allah! Ka roƙa mana Allah kada Ya azabtar da mu a ranar Alƙiyama saboda rashin kunya da munanan ɗabi’unmu a gare ka. Mu ne ya kamata mu yi maka hidima mu kuma bi umarninka.”
Sai Imam (A.S.) ya ce: “Na taɓa gwada haka a baya; duk lokacin da na yi tafiya tare da ayarin da suka san ni, ba sa barina in yi musu hidima. Saboda haka nake son in yi tafiya tare da ayarin da babu wanda ya san ni, domin in sami sa’ar yi wa Musulmi hidima.”
Ya Allah Ka Bamu Ikon Koyi Dasu.
Ina Tayaku Murnar Zagayowar Ranar Mauludin Imam Ali Zainul Abidin Assajjad (AS).
24/01/2026,
Comments
Post a Comment