Skip to main content

A Imanin mu (Mu 'yan shi'a) cewa: Allah mai hikima ne

A Imanin mu (Mu 'yan shi'a) cewa: Allah mai hikima ne, wannan yasa tun farkon duniya da ya ajiye mutum sai ya sanya kalifan shi a doron kasa, kalifanci shi kuma shine Adam, haka bayan Adam akwai wasiyyin shi Shisu har aka isa kan annabi Nuh haka har zuwa kan manzon Allah ba'ayi wani zamani da babu kalifan Allah a doron kasa ba; har muka iso zuwa wafatin manzo (S) manzo kuma ya kasance tun yana raye baya aiken mutane biyu face sai ya sanya mutum daya a cikin su ya zamo shugaba a tsakanin su, shin kunaga wanda yake yin haka zai bar duniya ba tare da ya sanya mai ci gaba da kula da mutane a bayan shi ba? Sai ya sanya Ali a matsayin wasiyyin shi da umurnin Allah, haka har zuwa kalifofi goma sha biyu a bayan shi har zuwa kan Imam Mahdi (atfs).

Kuma Allah cikin hikimar shi bazai bar qasa haka babu kalifan shi a doron ta ba, sai ya sanya na karshen su wato Imam Mahdi yayi dogon zamani, wanda har yanxu yana raye.

*ABIN DUBAWA*
Idan ya zama a doron kasa babu hujjar Allah to 'Dan adam zai iya zama yana da hujja akan Allah ranar qiyama, misali a yanxu haka da muke rayen nan babu wani Hujjan Allah dake raye, shi 'Dan adam zai sabi Allah ranar kiyama idan ubangiji yace mai yasa ka sabeni zaice ai baka bar Hujjar ka a doron kasa wanda zai zama shi muke komawa gare shi ba, shi kuma Imam Mahdi da zai shiga ghaiba sai ya sanya wasu da ake ce musu marji'ai ya zama ga su ake komawa a zamanin ghaibar Imam, kamar yadda yazo a hadith cewa:
 "Wanda ya kasance daga faqihai, mai iya kare kanshi ne, mai iya kiyaye addinin shi, mai 'Da'a wa al'amarin ubangijin shi, to ya zama wajibi ga sauran mutane su bishi".

A wajen 'yan Shi'a Ba'a taba yin wani zamani mai suna zamanin Jahiliyya ba, a kowane zamani 'yan shi'a suna da wanda zasu koma gareshi na abinda ya shafi addinin su, kodai wannan da zasu koma gare shi annabi ne ko kuma wasiyyin annabi ko kuma wanda annabi ya wakilta.

Wannan shine Imanin mu akan Imam Mahdi  (atfs).

Allah mun gode maka da ni'imar shi'anci.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...