Skip to main content

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam 
Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure:

1. Ilimi da Fahimta
> Imam Ali (a.s) yace:
"العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة."
al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm

 Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci.

Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta.


2. Ƙauna da Tausayi
> Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"رحم الله عبداً أعان ولده على برّه."
al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn

 Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).
 Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane.

3. Tarbiyya Mai Kyau
Imam Ali (a.s) yace:
"خيرُ ما ورّث الآباءُ الأبناءَ الأدب."
Nahj al-Balāgha, Hikma 399
> Ma’ana: Mafi alherin abin da iyaye ke gadarwa ‘ya’ya shi ne ladabi.
 Uwa ta gari tana ɗaukar tarbiyya a matsayin gadon da take barma ƴaƴanta koda bata raye zasu tashi a haka.


4. Haƙuri da Juriyar Rayuwa
> Imam Ali (a.s) yace:
"الصبرُ من الإيمانِ بمنزلةِ الرأسِ من الجسد، ولا إيمان لمن لا صبر له."
Nahj al-Balāgha, al-Hikmah 82

> Ma’ana: Haƙuri ga imani kamar kai ne ga jiki. Babu imani ga wanda babu haƙuri a tare da shi.
 Uwa ta gari tana jurewa wahalhalu cikin tawakkali da imani, wannan zaisa ƴaƴanta su taso masu haƙuri da juriya, ta yadda maza daga ƴaƴanta zasu zauna da matansu idan sunyi aure da hakuri, haka mata daga ciki.


5. Tsafta.
 Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"إن الله يحب الجمال والتجمل، ويكره البؤس والتباؤس."
Wasā’il al-Shīʿa, j.3, bāb nazāfat al-thawb

 Ma’ana: Lallai Allah yana son kyau da gyarawa, kuma yana ƙin datti da sakarcin gyara.
 Mace ta gari tana gyara gidanta da jikinta da kayan ‘ya’yanta, wannan din Allah na son haka.


6. Kulawa da Aure
Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"خيرُ نسائكم التي إذا خلت مع زوجها طرحت له ما يريده منها."
Wasā’il al-Shīʿa, j.14, bāb huqūq al-zawj

 Ma’ana: Mafi alherin matayenku ita ce wadda idan ta kasance tare da mijinta, ta kasance masa kamar yadda yake so.
 Uwa ta gari kuma matar aure ce ta kwarai, bata mu'amalar aure da wanin mijinta ko sabawa umurnin Allah a fili ko a ɓoye, domin idan ta kasance uwa ballagaza haka ƴaƴan zasu kasance.


7. Sanin Halayyar Yara da Tarbiyyar su
> Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"دع ابنك يلعب سبع سنين، ويؤدب سبع سنين، ولازمه سبع سنين، فإن أفلح، وإلا فإنّه من لا خير فيه."
Mustadrak al-Wasā’il, j.2

Ma’ana: Ka bar ɗanka ya yi wasa shekara 7, ka tarbiyyantar da shi shekara 7, sannan ka yi hulɗa da shi shekara 7. Idan ya gyaru, to daidai; idan ba haka ba, to babu alheri a cikinsa.
 Wannan ya nuna cewa tarbiyyar uwa dole ne ta zama bisa fahimta da lokaci, ta tsara musu lokacin karatu, lokacin wasa da lokacin bacci, kuma ta kebance lokacin zama da su domin jin halin da suke ciki. 


Matar da ta tare waɗannan ita ake kira uwa ta gari, kuma mata ta gari.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan.

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan. A lokacin da Sayyid Muhammad Baƙir Sadr yake neman ilimi Ƙanwarsa Bintul Hudah tace: "Na kasance tare da ɗan'uwana a wancan lokacin muna tattara kuɗin da muke samu, koda kuwa kaɗan ne, sai Sayyid ya sayi littafi da su, mu karanta mu fahimta. Daga baya sai ya sayar da littafin domin ya sayi wani. Haka muka ci gaba da rayuwa bayan hijirarmu zuwa Najaf al-Ashraf" - Amma daga ƙarshe mai ya faru? Ilimin shi Sayyid Muhammad Baƙir Sadr (QS) da rubuce rubucen shi sun gajiyar da masu bincike, saboda duk wani mai ilimi da ya karanta littattafansa sai ya jinjina masa, ga kaɗan daga shaidan manyan Malaman Shi'a a kansa: - Ayatullah Al-ʿUzma Sayyid Abul Qasim Al-Khuʾi (QS) yace: "Lallai Najaful Ashraf tana alfahari da Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr. Lallai Allah Maɗaukaki Ya bai wa wannan Sayyid abin da bai ba wa wani ɗalibina ba." - Sayyid Ruhullah Al-Musawi Al-Khumaini (QS) yace: "Sayyid Muhammad Baqir Sadr yana daga cikin fitattun M...