Skip to main content

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam 
Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure:

1. Ilimi da Fahimta
> Imam Ali (a.s) yace:
"العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة."
al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm

 Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci.

Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta.


2. Ƙauna da Tausayi
> Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"رحم الله عبداً أعان ولده على برّه."
al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn

 Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).
 Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane.

3. Tarbiyya Mai Kyau
Imam Ali (a.s) yace:
"خيرُ ما ورّث الآباءُ الأبناءَ الأدب."
Nahj al-Balāgha, Hikma 399
> Ma’ana: Mafi alherin abin da iyaye ke gadarwa ‘ya’ya shi ne ladabi.
 Uwa ta gari tana ɗaukar tarbiyya a matsayin gadon da take barma ƴaƴanta koda bata raye zasu tashi a haka.


4. Haƙuri da Juriyar Rayuwa
> Imam Ali (a.s) yace:
"الصبرُ من الإيمانِ بمنزلةِ الرأسِ من الجسد، ولا إيمان لمن لا صبر له."
Nahj al-Balāgha, al-Hikmah 82

> Ma’ana: Haƙuri ga imani kamar kai ne ga jiki. Babu imani ga wanda babu haƙuri a tare da shi.
 Uwa ta gari tana jurewa wahalhalu cikin tawakkali da imani, wannan zaisa ƴaƴanta su taso masu haƙuri da juriya, ta yadda maza daga ƴaƴanta zasu zauna da matansu idan sunyi aure da hakuri, haka mata daga ciki.


5. Tsafta.
 Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"إن الله يحب الجمال والتجمل، ويكره البؤس والتباؤس."
Wasā’il al-Shīʿa, j.3, bāb nazāfat al-thawb

 Ma’ana: Lallai Allah yana son kyau da gyarawa, kuma yana ƙin datti da sakarcin gyara.
 Mace ta gari tana gyara gidanta da jikinta da kayan ‘ya’yanta, wannan din Allah na son haka.


6. Kulawa da Aure
Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"خيرُ نسائكم التي إذا خلت مع زوجها طرحت له ما يريده منها."
Wasā’il al-Shīʿa, j.14, bāb huqūq al-zawj

 Ma’ana: Mafi alherin matayenku ita ce wadda idan ta kasance tare da mijinta, ta kasance masa kamar yadda yake so.
 Uwa ta gari kuma matar aure ce ta kwarai, bata mu'amalar aure da wanin mijinta ko sabawa umurnin Allah a fili ko a ɓoye, domin idan ta kasance uwa ballagaza haka ƴaƴan zasu kasance.


7. Sanin Halayyar Yara da Tarbiyyar su
> Imam al-Sadiq (a.s) yace:
"دع ابنك يلعب سبع سنين، ويؤدب سبع سنين، ولازمه سبع سنين، فإن أفلح، وإلا فإنّه من لا خير فيه."
Mustadrak al-Wasā’il, j.2

Ma’ana: Ka bar ɗanka ya yi wasa shekara 7, ka tarbiyyantar da shi shekara 7, sannan ka yi hulɗa da shi shekara 7. Idan ya gyaru, to daidai; idan ba haka ba, to babu alheri a cikinsa.
 Wannan ya nuna cewa tarbiyyar uwa dole ne ta zama bisa fahimta da lokaci, ta tsara musu lokacin karatu, lokacin wasa da lokacin bacci, kuma ta kebance lokacin zama da su domin jin halin da suke ciki. 


Matar da ta tare waɗannan ita ake kira uwa ta gari, kuma mata ta gari.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...