Skip to main content

Jirgin Tsira! Meka Sani Game Da Jirgin Tsira!

Jirgin Tsira! Meka Sani Game Da Jirgin Tsira!

Allah maɗaukakin sarki yana cewa:

وَقَالَ ارْكَبُوا فِيهَا بِسْمِ اللَّهِ مَجْرَاهَا وَمُرْسَاهَا ۚ إِنَّ رَبِّي لَغَفُورٌ رَّحِيمٌ

Me Tafsirul-Amsal yace:
Tsira daga ɗufana baya taɓa yiwuwa ba tare da jirgin tsira (Safinat-Annajati) ba, ba sharaɗi bane sai wannan jirgi ya zamto na katako ko ƙarfe ba, amma me yafi kyau ace wannan jirgi ya zamto addini dake kula da ɗabi'u, kuma ya bada rayuwa Kyakykyawan rayuwa,  kuma yayi juriya tare da tsayawa ƙyam a yayin da ruwan ɗufanan karkacewan fikira ya rinƙa tashi sama yana dawowa ƙasa, daga ƙarshe ya isar da mabiyan sa zuwa bakin tafki na Safinat-Annajati.

A bisa wannan ne aka samu ruwayoyi dayawa daga Annabi (S) a littafin shi'a da sunnah dake nuna Ahlul-baitin sa - Imaman shiriya - masu kare addini - cewa sune (Safinatun najati) jirgin tsira nan.

Abu Zaar ya kasance jingine da ɗakin ka'aba yake cewa: "Nine Abuzarr Algiffari, wanda bai sanni ba nine jundub sahabin manzon Allah (S) naji ma'aikin Allah (S) yana cewa: (Misalin Ahlubaiti na misalin jirgin Annabi Nuhu ne, wanda ya hau ya tsira)
A wani ruwayan kuma an ƙara da cewa: (Wanda ya barta ya nutse) ko kuma (wanda ya barta ya halaka).

Wannan hadisi mai girma daga Annabi (S) da saraha yake bayyana mana cewa: a duk sanda ruwan ɗufana na fikiran zamantakewa ko na Aƙida ya ƙwace a tsakanin al'ummar musulmi, tofa hanyar tsira ɗaya tilo itace komawa ga mazhabin Ahlulbaiti (AS), ba komawa mazhabin da mahukuntan da suka gabata suka ƙirƙira ba, wacce bata da wani alaƙa ta kusa kota nesa da Ahlulbaiti (AS).

Kulasar Magana:
Allah maɗaukakin sarki bisa luɗufin sa da ya halicci mutum sai ya sanya masa hanyar tsira, ya aiko Annabawa da manzanni duka domin su nunawa mutum hanyar tsira, wanda idan ya riƙa ya tsira, idan yaƙi ya halaka, to wannan hanya ba komai bace face ruƙo da Alkur'ani da Ahlulbaiti (AS) (Shi yasa Annabi ya kira su da suna jirgin Nuhu, kuma nauyaya biyu) wanda duk yayi ruƙo dasu ya tsira duniya da lahira.

Ya Allah ka tabbatar damu akan yin ruƙo da waɗan nan tsarkaka.

©24/04/2023.
E m r a n   D a r u s s a l a m.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...