Skip to main content

Jirgin Tsira! Meka Sani Game Da Jirgin Tsira!

Jirgin Tsira! Meka Sani Game Da Jirgin Tsira!

Allah maɗaukakin sarki yana cewa:

وَقَالَ ارْكَبُوا فِيهَا بِسْمِ اللَّهِ مَجْرَاهَا وَمُرْسَاهَا ۚ إِنَّ رَبِّي لَغَفُورٌ رَّحِيمٌ

Me Tafsirul-Amsal yace:
Tsira daga ɗufana baya taɓa yiwuwa ba tare da jirgin tsira (Safinat-Annajati) ba, ba sharaɗi bane sai wannan jirgi ya zamto na katako ko ƙarfe ba, amma me yafi kyau ace wannan jirgi ya zamto addini dake kula da ɗabi'u, kuma ya bada rayuwa Kyakykyawan rayuwa,  kuma yayi juriya tare da tsayawa ƙyam a yayin da ruwan ɗufanan karkacewan fikira ya rinƙa tashi sama yana dawowa ƙasa, daga ƙarshe ya isar da mabiyan sa zuwa bakin tafki na Safinat-Annajati.

A bisa wannan ne aka samu ruwayoyi dayawa daga Annabi (S) a littafin shi'a da sunnah dake nuna Ahlul-baitin sa - Imaman shiriya - masu kare addini - cewa sune (Safinatun najati) jirgin tsira nan.

Abu Zaar ya kasance jingine da ɗakin ka'aba yake cewa: "Nine Abuzarr Algiffari, wanda bai sanni ba nine jundub sahabin manzon Allah (S) naji ma'aikin Allah (S) yana cewa: (Misalin Ahlubaiti na misalin jirgin Annabi Nuhu ne, wanda ya hau ya tsira)
A wani ruwayan kuma an ƙara da cewa: (Wanda ya barta ya nutse) ko kuma (wanda ya barta ya halaka).

Wannan hadisi mai girma daga Annabi (S) da saraha yake bayyana mana cewa: a duk sanda ruwan ɗufana na fikiran zamantakewa ko na Aƙida ya ƙwace a tsakanin al'ummar musulmi, tofa hanyar tsira ɗaya tilo itace komawa ga mazhabin Ahlulbaiti (AS), ba komawa mazhabin da mahukuntan da suka gabata suka ƙirƙira ba, wacce bata da wani alaƙa ta kusa kota nesa da Ahlulbaiti (AS).

Kulasar Magana:
Allah maɗaukakin sarki bisa luɗufin sa da ya halicci mutum sai ya sanya masa hanyar tsira, ya aiko Annabawa da manzanni duka domin su nunawa mutum hanyar tsira, wanda idan ya riƙa ya tsira, idan yaƙi ya halaka, to wannan hanya ba komai bace face ruƙo da Alkur'ani da Ahlulbaiti (AS) (Shi yasa Annabi ya kira su da suna jirgin Nuhu, kuma nauyaya biyu) wanda duk yayi ruƙo dasu ya tsira duniya da lahira.

Ya Allah ka tabbatar damu akan yin ruƙo da waɗan nan tsarkaka.

©24/04/2023.
E m r a n   D a r u s s a l a m.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan.

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan. A lokacin da Sayyid Muhammad Baƙir Sadr yake neman ilimi Ƙanwarsa Bintul Hudah tace: "Na kasance tare da ɗan'uwana a wancan lokacin muna tattara kuɗin da muke samu, koda kuwa kaɗan ne, sai Sayyid ya sayi littafi da su, mu karanta mu fahimta. Daga baya sai ya sayar da littafin domin ya sayi wani. Haka muka ci gaba da rayuwa bayan hijirarmu zuwa Najaf al-Ashraf" - Amma daga ƙarshe mai ya faru? Ilimin shi Sayyid Muhammad Baƙir Sadr (QS) da rubuce rubucen shi sun gajiyar da masu bincike, saboda duk wani mai ilimi da ya karanta littattafansa sai ya jinjina masa, ga kaɗan daga shaidan manyan Malaman Shi'a a kansa: - Ayatullah Al-ʿUzma Sayyid Abul Qasim Al-Khuʾi (QS) yace: "Lallai Najaful Ashraf tana alfahari da Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr. Lallai Allah Maɗaukaki Ya bai wa wannan Sayyid abin da bai ba wa wani ɗalibina ba." - Sayyid Ruhullah Al-Musawi Al-Khumaini (QS) yace: "Sayyid Muhammad Baqir Sadr yana daga cikin fitattun M...