Skip to main content

ZAI FANSHE KA DAGA ABUBUWAN TSORON DAKE CIKIN RAYUWAR BARZAKH.

ZAI FANSHE KA DAGA ABUBUWAN TSORON DAKE CIKIN RAYUWAR BARZAKH.

An hakaito cewa "Wani Malami daga cikin ٓٓArifai yake cewa: "Na kasance ina da Maqoci sai wannan maqoci nawa ya koma ga ubangijin sa, Bayan wasu kwanaki da wafatin sa kwatsam sai na ganshi a mafarki na,Saina tambaye shi cewa ya ka samu kanka a can (Rayuwar barzakh)?
Sai yace dani: ya sayyadi wlh naga Musiba da manya manyan abin tsoro, Masamman lokacin da Mala'iku guda biyu (munkar da nakir) suka zomin, Suka fara min tambayoyi masu yawa, amma ni ban iya amsa musu tambayoyin da suke min ba, sbd na rasa ikon yin magana a daidai wannan lokacin (Harshena ya kasa motsawa na zama kamar kurma)  Sai nace a raina:
Niko na shiga uku, wannan wane irin axaba ne mai girma?
Shin ban kasance Mu'umini a rayuwata ba?
Ko ban mutu ina musulmi ba?
Mala'ikun nan suka tsananta akaina da tambayoyi kuma ni na kasa basu amsa, a daidai wannan lokaci kwatsam saiga wani kyakykyawan saurayi ya bayyana, Mai sanye da kanshi, Sai kawai ya shiga tsakanina da wadannan mala'iku guda biyu, Sai ya fara gayamin duk wani amsar tambaya da sukayi min ina amsawa, Sai nace dashi " Rahamar Allah a gareka waye kai"?
Lallai ka ceceni daga azaba mai girma.
Sai Saurayin nan yace: "Ni Mutum ne da aka halitta daga salatin da ka kasance kanayi a rayuwarka ta duniya kana aika wannan salatin ga annabi (S) da iyalan gidansa" 
Sai abin ya bani mamaki, nace inama da da yawan salati na gama rayuwata daga farkon ta zuwa karshen ta.

Annabi Muhammad (S) ya kasance yana cewa; "Ku yawaita salati a gareni, domin salatin ku a gareni haske ce a cikin qabarin ku, Kuma haske ce akan siradi yayin tsallakawar ku,kuma haske ce a cikin Aljannah"

قد أفلح من صلّى على محمد و آل محمد.
اللهم صل على محمد و آل محمد

Dan uwan ku Imran Darussalam, Allah yasa mu amfana tare da bamu ikon yawaita salati ga manzo (s) da Ahlul-baiti (AS).

28/April/2018
imrandarussalam99@gmail.com

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...