Skip to main content

ZAI FANSHE KA DAGA ABUBUWAN TSORON DAKE CIKIN RAYUWAR BARZAKH.

ZAI FANSHE KA DAGA ABUBUWAN TSORON DAKE CIKIN RAYUWAR BARZAKH.

An hakaito cewa "Wani Malami daga cikin ٓٓArifai yake cewa: "Na kasance ina da Maqoci sai wannan maqoci nawa ya koma ga ubangijin sa, Bayan wasu kwanaki da wafatin sa kwatsam sai na ganshi a mafarki na,Saina tambaye shi cewa ya ka samu kanka a can (Rayuwar barzakh)?
Sai yace dani: ya sayyadi wlh naga Musiba da manya manyan abin tsoro, Masamman lokacin da Mala'iku guda biyu (munkar da nakir) suka zomin, Suka fara min tambayoyi masu yawa, amma ni ban iya amsa musu tambayoyin da suke min ba, sbd na rasa ikon yin magana a daidai wannan lokacin (Harshena ya kasa motsawa na zama kamar kurma)  Sai nace a raina:
Niko na shiga uku, wannan wane irin axaba ne mai girma?
Shin ban kasance Mu'umini a rayuwata ba?
Ko ban mutu ina musulmi ba?
Mala'ikun nan suka tsananta akaina da tambayoyi kuma ni na kasa basu amsa, a daidai wannan lokaci kwatsam saiga wani kyakykyawan saurayi ya bayyana, Mai sanye da kanshi, Sai kawai ya shiga tsakanina da wadannan mala'iku guda biyu, Sai ya fara gayamin duk wani amsar tambaya da sukayi min ina amsawa, Sai nace dashi " Rahamar Allah a gareka waye kai"?
Lallai ka ceceni daga azaba mai girma.
Sai Saurayin nan yace: "Ni Mutum ne da aka halitta daga salatin da ka kasance kanayi a rayuwarka ta duniya kana aika wannan salatin ga annabi (S) da iyalan gidansa" 
Sai abin ya bani mamaki, nace inama da da yawan salati na gama rayuwata daga farkon ta zuwa karshen ta.

Annabi Muhammad (S) ya kasance yana cewa; "Ku yawaita salati a gareni, domin salatin ku a gareni haske ce a cikin qabarin ku, Kuma haske ce akan siradi yayin tsallakawar ku,kuma haske ce a cikin Aljannah"

قد أفلح من صلّى على محمد و آل محمد.
اللهم صل على محمد و آل محمد

Dan uwan ku Imran Darussalam, Allah yasa mu amfana tare da bamu ikon yawaita salati ga manzo (s) da Ahlul-baiti (AS).

28/April/2018
imrandarussalam99@gmail.com

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...