Skip to main content

Misali Mai Cike Da Darasi


Fitilar Ƙarshe...

Sayyid Ku'i (QS) a wani muhadarar sa cikin darasi a hauza yake cewa: "misali akwai wani birni da mutanen wannan birni ke rayuwa cikin duhu da hargitsi da karo da juna saboda tsananin duhu, amma kuma sarkin wannan gari mutum ne mai hikima, a binciken sa sai ya gano wata fitila da zata haskaka duka birnin, sai ya kawo wannan fitila ya sanya shi domin mutane su amfana da hasken sa, kowa yayi farin ciki (kan samun wannan fitila), amma bayan wasu ƴan kwanaki sai aka samu wasu suka jefi fitilar suka fasa shi, da yake sarkin garin mutum ne mai son al'ummar sa sai ya kawo wani fitilan daban ya sanya, suka ƙara fasa shi, ya ƙara sanyawa suka fasa, harta kaiga ya sanya fitilu goma sha ɗaya, amma suna fasawa, fitila ɗaya ce ta rage a gurin shi,
Shin ya ya kamata yayi?
Idan ya fito da ragowar wannan fitila mutanen gari zasu ƙara fasa shi su rayu (su) da zuriyar su cikin duhu.

Menene matsayar hikima da hankali a nan?
Hikima da hankali suna cewa: "Rashin sanya wannan fitila da bashi kulawa shine abinda yafi" wannan tasa sarki ya ɓoye fitila ɗaya tilo data rage, da nufin zai jira har zuwa ranar da mutane zasu hankalta su gane muhimmancin wannan fitila su amfana da hasken shi harma su iya bashi kariya.

Kamar hakane Allah ya sanya Imamai masu shiryarwa goma sha biyu, su fitilu ne masu haskaka wa, amma haka mutane suka rinƙa kashe su ɗaya bayan ɗaya, sai Allah ya ɓoye Imami na ƙarshen domin yana ji masa tsoro kuma saboda son da yake yiwa mutane, domin mutane su shiriya dashi, a yayin da zarafi ya bada hakan.

Ya Allah ka gaggauta bayyanar wanda zai haskaka wannan duniya da adalci bayan ta cika da zalunci wato Imam Mahadi (Atfs).

14 May 2023,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...