Skip to main content

Misali Mai Cike Da Darasi


Fitilar Ƙarshe...

Sayyid Ku'i (QS) a wani muhadarar sa cikin darasi a hauza yake cewa: "misali akwai wani birni da mutanen wannan birni ke rayuwa cikin duhu da hargitsi da karo da juna saboda tsananin duhu, amma kuma sarkin wannan gari mutum ne mai hikima, a binciken sa sai ya gano wata fitila da zata haskaka duka birnin, sai ya kawo wannan fitila ya sanya shi domin mutane su amfana da hasken sa, kowa yayi farin ciki (kan samun wannan fitila), amma bayan wasu ƴan kwanaki sai aka samu wasu suka jefi fitilar suka fasa shi, da yake sarkin garin mutum ne mai son al'ummar sa sai ya kawo wani fitilan daban ya sanya, suka ƙara fasa shi, ya ƙara sanyawa suka fasa, harta kaiga ya sanya fitilu goma sha ɗaya, amma suna fasawa, fitila ɗaya ce ta rage a gurin shi,
Shin ya ya kamata yayi?
Idan ya fito da ragowar wannan fitila mutanen gari zasu ƙara fasa shi su rayu (su) da zuriyar su cikin duhu.

Menene matsayar hikima da hankali a nan?
Hikima da hankali suna cewa: "Rashin sanya wannan fitila da bashi kulawa shine abinda yafi" wannan tasa sarki ya ɓoye fitila ɗaya tilo data rage, da nufin zai jira har zuwa ranar da mutane zasu hankalta su gane muhimmancin wannan fitila su amfana da hasken shi harma su iya bashi kariya.

Kamar hakane Allah ya sanya Imamai masu shiryarwa goma sha biyu, su fitilu ne masu haskaka wa, amma haka mutane suka rinƙa kashe su ɗaya bayan ɗaya, sai Allah ya ɓoye Imami na ƙarshen domin yana ji masa tsoro kuma saboda son da yake yiwa mutane, domin mutane su shiriya dashi, a yayin da zarafi ya bada hakan.

Ya Allah ka gaggauta bayyanar wanda zai haskaka wannan duniya da adalci bayan ta cika da zalunci wato Imam Mahadi (Atfs).

14 May 2023,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan.

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan. A lokacin da Sayyid Muhammad Baƙir Sadr yake neman ilimi Ƙanwarsa Bintul Hudah tace: "Na kasance tare da ɗan'uwana a wancan lokacin muna tattara kuɗin da muke samu, koda kuwa kaɗan ne, sai Sayyid ya sayi littafi da su, mu karanta mu fahimta. Daga baya sai ya sayar da littafin domin ya sayi wani. Haka muka ci gaba da rayuwa bayan hijirarmu zuwa Najaf al-Ashraf" - Amma daga ƙarshe mai ya faru? Ilimin shi Sayyid Muhammad Baƙir Sadr (QS) da rubuce rubucen shi sun gajiyar da masu bincike, saboda duk wani mai ilimi da ya karanta littattafansa sai ya jinjina masa, ga kaɗan daga shaidan manyan Malaman Shi'a a kansa: - Ayatullah Al-ʿUzma Sayyid Abul Qasim Al-Khuʾi (QS) yace: "Lallai Najaful Ashraf tana alfahari da Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr. Lallai Allah Maɗaukaki Ya bai wa wannan Sayyid abin da bai ba wa wani ɗalibina ba." - Sayyid Ruhullah Al-Musawi Al-Khumaini (QS) yace: "Sayyid Muhammad Baqir Sadr yana daga cikin fitattun M...