Skip to main content

Wahabiyanci A Mizani Part ( 1 ).


Wahabiyanci da wanda ya assasashi:
- Ana nasabta firƙan wahabiyya ne ga Muhammad bin Abdulwahab Bn Sulaiman Annajdi, wanda aka haifa a shekarar 1115 Hijiriyya, ya rasu a shekarar 1206 Hijiriyya.

Yayi karatun addini daidai gwargwado, kamar yadda a bayyane yake ya kasance mai yawan bibiya da muɗala'an labaran da suka shafi Musailama al-kazzab, da Sajah, da Aswadul Anasi, da Ɗulaiha Al-asadi, wanda tsatstsauran ra'ayin shi ya fara bayyana tun lokacin da yake karatu, mahaifin sa da wasu daga malaman sa su suka fara yaƙar wannan ra'ayi nashi, suka nuna a nisance shi, inda suke cewa: "Wannan zai ɓata, kuma zai ɓatar da dukkan waɗanda suka nisanci Allah kuma suka kasance shaƙiyyai".

A shekarar 1143 Hijiriyya ya bayyana da'awar sa zuwa ga sabuwar mazhabin sa, amma mahaifin sa da wasu daga malaman sa suka yi ƙoƙarin tsaida shi tare da tunkarar sa, suka karya karsashin kiran nasa, har zuwa lokacin da mahaifinsa ya rasu a shekarar 1153 Hijiriyya, a nanne ya samu damar jaddada da'awar sa tsakanin masu ƙarancin ilimi, da sauran mutane, aka samu dayawa daga cikin su suka bishi, nan mutanen garin suka taso kan shi (saboda yadda suka ga yana ɓatar da mutane) suka yi ƙoƙarin kashe shi, a lokacin ne ya gudu wani gari da ake kira (Uyainah), bayan zuwan shine ya samu kusantar sarkin Uyainah ya auri ƴar uwar sa, ya zauna a nan yana kira zuwa ga kanshi kuma zuwa ga bidi'ar sa, har ta kaiga ya ƙure haƙurin mutanen Uyainah suka kore shi daga garin, haka ya fita zuwa (Addar'iyyah) dake kan hanyar Najid.

Haka fikirar sa ta yaɗu a wannan gari har sarkin garin Muhammad bn Mas'ud ya zama daga mabiyan wannan tafiya tashi da sauran mutane, haka yaci gaba da tasarrufi kamar ma'abocin ijitihadi muɗlaqa, domin kuwa bai kasance yana ɗaukan fatwan magabata (Salaf) ba, kuma baya ɗaukan fatwan faƙihan zamanin sa, dukda a haƙiƙanin gaskiya bayyi karatun da ya kaishi ga ijitihadi ba.

Amma ɗan uwan sa Sheikh Sulaiman bn Abdulwahab ya sifanta shi, wanda shi yafi kowa sanin sa, wanda ya kaiga rubuta littafi guda domin ɓata kiran ɗan uwan shi da tabbatar da hatsarin ta tsakanin al'umma, kamar yadda yazo a wani ibaara inda yake bayyana ta'arifin wahabiyya da wanda ya assasa ta, inda yake cewa: "A yau an jarabci mutane da wanda ke intisaabi zuwa ga kitabu wassunnah, yana istinbaɗi (tsamo hukunce-hukunce) a cikin ta ba tare da ya damu ba, wanda ya saɓa dashi a ra'ayi sunan shi kafuri, wanda kuma a haƙiƙanin gaskiya babu wani alama na ijitihadi data bayyana tare dashi, amma dukda haka ya saye ƙwaƙwalen dayawa daga jahilai, innalillahi wa inna ilaihi raji'un".

Masdar: zaka samu duka wannan da ƙarin bayani a:

- تاريخ نجد لمحمود شكري الآلوسي.
- الصواعق الإلهية في الرد على الوهابية للشيخ سليمان بن عبد الوهاب.
- فتنة الوهابية.

20 May 2022.
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...