Skip to main content

Wahabiyanci A Mizani Part ( 4 )



- Wahabiyawa da sauran musulmi (Bidi'ar wahabiyawa mai girma).

- Yana daga Aƙidar wahabiyawa cewa: sunyi imani cewa: su kaɗai ne ma'abota tauhidi tsantsa, amma sauran musulmai waɗanda basu ba mushrikai ne, kuma jinin su da dukiyar su ya halasta, sannan sun halasta a yaƙe su, sannan koda sun furta kalmar nan ta (La'ilaaha illallah Muhammad rasulullah) bata wadatarwa, muddin dai sunyi imani da tabarruki da ƙabarin manzon Allah (S) - suna nufin ziyarar sa da neman ceton sa - shi yasa suke cewa: duk musulmin da yayi imani da ziyaran ƙabari koda na manzon Allah Muhammad (S) ne mushriki ne, kuma shirkan sa tafi na mutanen jahiliyya masu bautan gumaka tsanani.
Zaku samu wannan i'itiƙadi nasu a manyan-manyan litattafan su kamar:
- الرسائل العملية التسع لمحمد بن عبد الوهاب : 79.
- تطهير الإعتقاد للصنعاني : 7، 12 ، 35.
- فتح المجيد : 40 - 41.
- ورسالة أربع القواعد.
-  ورسالة كشف الشبهات لمحمد بن عبد الوهاب ، وغيرها ).

- Haka nan idan ka duba shi wannan littafi na كشف الشبهات zaka ga inda Muhammad bn Abdulwahab da kansa yake  furta kalmar shirka da mushirkai akan dukkan musulmai (banda mabiyan sa) a guri 24.
- Haka nan a cikin wannan littafi ya kira musulmai da suna kafirai, masu bautan gumaka, masu ridda, marasa tauhidi, kuma maƙiya Allah, masu iddi'a'in musulunci a guri 20.

Tambaya ta anan itace kamar haka: "Shin wannan aƙida ta kafirta dukkan musulmai an samo tane daga magabata (salaf) ko bidi'a ce sabuwa da suka ƙirƙira?

- Ibn Taimiyya dai yana cewa: "Bana kafirta musulmai da zunubin da suka kasance suna aikatawa, koda akan ijitihadi ne sai khawarijh kaɗai.
Duba littafin sa mai suna:
- مجموعة فتاوى إبن تيمية 20:13

Kulasar Rubutun Shin: Su wahabiyawa a wajen su dukkan wani musulmin da basu ba to mushriki ne kafiri, sawa'un yayi imani da ziyaran ƙabarin manzon Allah da neman ceton sa ko bayyi ba, wanda kuwa yayi imani da ziyarar ƙabarin manzon Allah da yin tawassuli dashi to shi bayan ya kafirta jinin shi da dukiyan shi sun halasta a sheƙar dasu.

Duk bawahabiyen da kaga yana zama da kai yana sakar maka fuska, to taƙiyya ce yake yi maka, amma a haƙiƙanin gaskiya ganin tataccen kafuri yake maka, ta yanda da zai samu dama zai iya kashe ka, ya lalata maka dukiyar ka, zaka iya gane haka ta idan kayi wani abu suce maka ɗan bidi'a, ko ɗan gargajiya ba komai hake ke nufi ba face: "wanda bashi da addini" wanda bashi da addini kuma sunan sa...

A janibin yaƙarka da lalata maka dukiya da kwantar da kai su yanka kuwa (Boko haram, ISIS, Taliban) sun ishe ka misali.

23 May 2023,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...