Skip to main content

Wahabiyanci A Mizani Part ( 4 )



- Wahabiyawa da sauran musulmi (Bidi'ar wahabiyawa mai girma).

- Yana daga Aƙidar wahabiyawa cewa: sunyi imani cewa: su kaɗai ne ma'abota tauhidi tsantsa, amma sauran musulmai waɗanda basu ba mushrikai ne, kuma jinin su da dukiyar su ya halasta, sannan sun halasta a yaƙe su, sannan koda sun furta kalmar nan ta (La'ilaaha illallah Muhammad rasulullah) bata wadatarwa, muddin dai sunyi imani da tabarruki da ƙabarin manzon Allah (S) - suna nufin ziyarar sa da neman ceton sa - shi yasa suke cewa: duk musulmin da yayi imani da ziyaran ƙabari koda na manzon Allah Muhammad (S) ne mushriki ne, kuma shirkan sa tafi na mutanen jahiliyya masu bautan gumaka tsanani.
Zaku samu wannan i'itiƙadi nasu a manyan-manyan litattafan su kamar:
- الرسائل العملية التسع لمحمد بن عبد الوهاب : 79.
- تطهير الإعتقاد للصنعاني : 7، 12 ، 35.
- فتح المجيد : 40 - 41.
- ورسالة أربع القواعد.
-  ورسالة كشف الشبهات لمحمد بن عبد الوهاب ، وغيرها ).

- Haka nan idan ka duba shi wannan littafi na كشف الشبهات zaka ga inda Muhammad bn Abdulwahab da kansa yake  furta kalmar shirka da mushirkai akan dukkan musulmai (banda mabiyan sa) a guri 24.
- Haka nan a cikin wannan littafi ya kira musulmai da suna kafirai, masu bautan gumaka, masu ridda, marasa tauhidi, kuma maƙiya Allah, masu iddi'a'in musulunci a guri 20.

Tambaya ta anan itace kamar haka: "Shin wannan aƙida ta kafirta dukkan musulmai an samo tane daga magabata (salaf) ko bidi'a ce sabuwa da suka ƙirƙira?

- Ibn Taimiyya dai yana cewa: "Bana kafirta musulmai da zunubin da suka kasance suna aikatawa, koda akan ijitihadi ne sai khawarijh kaɗai.
Duba littafin sa mai suna:
- مجموعة فتاوى إبن تيمية 20:13

Kulasar Rubutun Shin: Su wahabiyawa a wajen su dukkan wani musulmin da basu ba to mushriki ne kafiri, sawa'un yayi imani da ziyaran ƙabarin manzon Allah da neman ceton sa ko bayyi ba, wanda kuwa yayi imani da ziyarar ƙabarin manzon Allah da yin tawassuli dashi to shi bayan ya kafirta jinin shi da dukiyan shi sun halasta a sheƙar dasu.

Duk bawahabiyen da kaga yana zama da kai yana sakar maka fuska, to taƙiyya ce yake yi maka, amma a haƙiƙanin gaskiya ganin tataccen kafuri yake maka, ta yanda da zai samu dama zai iya kashe ka, ya lalata maka dukiyar ka, zaka iya gane haka ta idan kayi wani abu suce maka ɗan bidi'a, ko ɗan gargajiya ba komai hake ke nufi ba face: "wanda bashi da addini" wanda bashi da addini kuma sunan sa...

A janibin yaƙarka da lalata maka dukiya da kwantar da kai su yanka kuwa (Boko haram, ISIS, Taliban) sun ishe ka misali.

23 May 2023,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan.

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan. A lokacin da Sayyid Muhammad Baƙir Sadr yake neman ilimi Ƙanwarsa Bintul Hudah tace: "Na kasance tare da ɗan'uwana a wancan lokacin muna tattara kuɗin da muke samu, koda kuwa kaɗan ne, sai Sayyid ya sayi littafi da su, mu karanta mu fahimta. Daga baya sai ya sayar da littafin domin ya sayi wani. Haka muka ci gaba da rayuwa bayan hijirarmu zuwa Najaf al-Ashraf" - Amma daga ƙarshe mai ya faru? Ilimin shi Sayyid Muhammad Baƙir Sadr (QS) da rubuce rubucen shi sun gajiyar da masu bincike, saboda duk wani mai ilimi da ya karanta littattafansa sai ya jinjina masa, ga kaɗan daga shaidan manyan Malaman Shi'a a kansa: - Ayatullah Al-ʿUzma Sayyid Abul Qasim Al-Khuʾi (QS) yace: "Lallai Najaful Ashraf tana alfahari da Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr. Lallai Allah Maɗaukaki Ya bai wa wannan Sayyid abin da bai ba wa wani ɗalibina ba." - Sayyid Ruhullah Al-Musawi Al-Khumaini (QS) yace: "Sayyid Muhammad Baqir Sadr yana daga cikin fitattun M...