Skip to main content

Wahabiyanci A Mizani Part ( 5 )



- Wahabiyawa Da Khawarijh.

- Wani abin da zai baka mamaki shine: idan ka duba da kyau zaka ga yadda kamanceceniya yake tsakanin Wahabiyawa da Khawarijawa ta yadda suka karkace daga sauran al'ummar musulmi, ga kaɗan daga inda suke kama:

1 - Khawarijawa sun saɓa da dukkan musulmi inda suke cewa: "Haƙiƙa wanda ya aikata kabira kafiri ne, haka nan wahabiyawa suma sun kafirta duka musulmin da basu ba akan kabira. 
Duba littafin:
- كشف الشبهات لمحمد بن عبد الوهاب.
- تطهير الإعتقاد للصنعاني.

2 - Khawarijawa sun fitar da hukuncin cewa: "Dukkan gidan da ake aikata kabaa'ir  ya halasta a yaƙi wannan gidan (Ai jinin su ya halasta da dukiyar su, haka Wahabiyawa suka fidda hukunci cewa a yaƙi gidan da ake aikata kabaa'ir, jini da dukiyar su ya halasta a sheƙar dashi.

3 - Wahabiyawa suna kama da Khawarijawa wajen tsanani cikin addini da daskarewa cikin fahimtar addinin, Khawarijawa a yayin da suka karanta fadin Allah cewa: (إن الحكم إلا لله) sai suka ce: wanda ya halasta hukunci haƙiƙa mushriki ne, sai suka ɗau shi'aar ɗin su ta zamo (لا حكم إلا لله) ai babu wani hukunci sai na Allah كلمة حق يراد بها الباطل  wannan magana nasu daskarewa ne da jahilci mai girma, a haƙiƙanin gaskiya shi hukunci abune tabbatacce a cikin Alkur'ani mai girma da hadith da siran manzo (S) da Ahlulbaiti (AS) da Sahabbai managarta, Haka nan wahabiyawa a yayin da suka karanta faɗin Allah: (إياك نعبد وإياك نستعين) ai (a gareka muke bauta kuma a gareka muke neman taimako) da ayar nan (من ذا الذي يشفع عنده إلا بإذنه) ai (Wane ne wanda yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa?) Da ayar nan da yake cewa: (لا يشفعون إلا لمن إرتضى) 
Suke cewa: duk wanda ya halasta neman ceto a wajen Annabi (S) da salihai haƙiƙa yayi shirka wa Allah, wanda kuma ya nufi ziyartan Annabi (S) ko kuma ya nemi ceto a gurin shi to haƙiƙa ya riƙi wani Ubangijin daba Allah ba, su kuma shi'aar ɗin su shine: 
لا معبود إلا الله، ولا شفاعة إلا لله
Babu abin bautawa sai Allah, Babu ceto sai a gurin Allah.
Wannan shine
 كلمة حق يراد بها الباطل.
- Zaku fahimci hakane idan kuka saurari maganar Dr na bauchi Dr. Idris Tanshi, ai a cikin maganar shi cewa yayi ko manzon Allah basa neman taimakon sa, kuma haka haƙiƙanin Aƙidar tasu take, na raina shugaba rasulullah (S).

4 - Ibn Taimiyya yace: "Khawarij sune farkon bidi'a da suka fara bayyana a musulunci, suka kafirta ma'abota musulunci suka halasta jinin su).
 - مجموعة فتاوى 20:13.

4 - Hadisan da suka zo kan Khawarijh wasu daga ciki sun ɗabbaƙu akan wahabiyawa...
- Yazo a hadisi cewa: "Daga gabashin ƙasa wasu mutane zasu bayyana, masu karanta Alkur'ani, suna ficewa daga addini kamar yadda kwari yake fita daga cikin baka, wannan itace alamar su"
Yana cikin:
صحيح البخاري - كتاب التوحيد.

Al-ƙisɗalani a sharhin wannan hadisi yake cewa:
(من قبل المشرق أي من جهة شرق المدينة كنجد وما بعدها)
(Ta ɓangaren gabashi ai ta jihhar gabashin madina - kamar najadu da bayan ta).
- Najadu shine matattaran wahabiyawa kuma tushen su na farko wanda daga nan dukka fitinar wahabiyya take fitowa...
Shi yasa malaman zamani sukace: babu buƙatan wallafa littafi domin yin raddi wa wahabiyawa, ya isa ka fito ka bayyana alamomin su, domin su kan su basaso a rinƙa bayyana alamun nasu.

5 - Yazo a hadisi dake sifanta siffofin khawarij cewa: (Suna kashe ma'abota musulunci suyi iddi'a'in cewa ma'abota bautan gumaka ne).
Ibn Taimiyya ma ya kawo a littafin sa.
- Wannan shine sifa da halin wahabiyawa, basa cinna wutar fitina da yaƙi da kisa sai akan ma'abota fuskantar alƙibla, a tarihi babu inda aka kawo tarihin cewa sun yaƙi masu bautan gumaka, kai a cikin littafinsu ma babu tunkarar masu bautan gumaka.

6 - Bukhari ya kawo daga ibn umar a siffanta Khawarijawa cewa: (Haƙiƙa su sun ɗauki wannan ayoyi da ta sauƙa akan kafirai, suka sanya ta akan muminai).
- Duba:
- صحيح البخاري - كتاب إستتابة المرتدين - باب 5)

- A wani ruwayan kuma:, yazo daga Ibn Abbas yace: (Kada ku zamto kamar Khawarijawa, sunyi tawilin ayoyin Alkur'ani akan ma'abota alƙibla, haƙiƙa wannan ayoyi ta sauƙa ne akan Ahlul-kitabi da mushrikai, suka sanya akan su (akan musulmai) suka sheƙar da jini, suka halasta dukiyar su).

Wadannan fa sune wahabiyawa, Ya Allah kayi mana tsari dasu.

24 May 2023,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...