Skip to main content

Wahabiyanci A Mizani Part ( 5 )



- Wahabiyawa Da Khawarijh.

- Wani abin da zai baka mamaki shine: idan ka duba da kyau zaka ga yadda kamanceceniya yake tsakanin Wahabiyawa da Khawarijawa ta yadda suka karkace daga sauran al'ummar musulmi, ga kaɗan daga inda suke kama:

1 - Khawarijawa sun saɓa da dukkan musulmi inda suke cewa: "Haƙiƙa wanda ya aikata kabira kafiri ne, haka nan wahabiyawa suma sun kafirta duka musulmin da basu ba akan kabira. 
Duba littafin:
- كشف الشبهات لمحمد بن عبد الوهاب.
- تطهير الإعتقاد للصنعاني.

2 - Khawarijawa sun fitar da hukuncin cewa: "Dukkan gidan da ake aikata kabaa'ir  ya halasta a yaƙi wannan gidan (Ai jinin su ya halasta da dukiyar su, haka Wahabiyawa suka fidda hukunci cewa a yaƙi gidan da ake aikata kabaa'ir, jini da dukiyar su ya halasta a sheƙar dashi.

3 - Wahabiyawa suna kama da Khawarijawa wajen tsanani cikin addini da daskarewa cikin fahimtar addinin, Khawarijawa a yayin da suka karanta fadin Allah cewa: (إن الحكم إلا لله) sai suka ce: wanda ya halasta hukunci haƙiƙa mushriki ne, sai suka ɗau shi'aar ɗin su ta zamo (لا حكم إلا لله) ai babu wani hukunci sai na Allah كلمة حق يراد بها الباطل  wannan magana nasu daskarewa ne da jahilci mai girma, a haƙiƙanin gaskiya shi hukunci abune tabbatacce a cikin Alkur'ani mai girma da hadith da siran manzo (S) da Ahlulbaiti (AS) da Sahabbai managarta, Haka nan wahabiyawa a yayin da suka karanta faɗin Allah: (إياك نعبد وإياك نستعين) ai (a gareka muke bauta kuma a gareka muke neman taimako) da ayar nan (من ذا الذي يشفع عنده إلا بإذنه) ai (Wane ne wanda yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa?) Da ayar nan da yake cewa: (لا يشفعون إلا لمن إرتضى) 
Suke cewa: duk wanda ya halasta neman ceto a wajen Annabi (S) da salihai haƙiƙa yayi shirka wa Allah, wanda kuma ya nufi ziyartan Annabi (S) ko kuma ya nemi ceto a gurin shi to haƙiƙa ya riƙi wani Ubangijin daba Allah ba, su kuma shi'aar ɗin su shine: 
لا معبود إلا الله، ولا شفاعة إلا لله
Babu abin bautawa sai Allah, Babu ceto sai a gurin Allah.
Wannan shine
 كلمة حق يراد بها الباطل.
- Zaku fahimci hakane idan kuka saurari maganar Dr na bauchi Dr. Idris Tanshi, ai a cikin maganar shi cewa yayi ko manzon Allah basa neman taimakon sa, kuma haka haƙiƙanin Aƙidar tasu take, na raina shugaba rasulullah (S).

4 - Ibn Taimiyya yace: "Khawarij sune farkon bidi'a da suka fara bayyana a musulunci, suka kafirta ma'abota musulunci suka halasta jinin su).
 - مجموعة فتاوى 20:13.

4 - Hadisan da suka zo kan Khawarijh wasu daga ciki sun ɗabbaƙu akan wahabiyawa...
- Yazo a hadisi cewa: "Daga gabashin ƙasa wasu mutane zasu bayyana, masu karanta Alkur'ani, suna ficewa daga addini kamar yadda kwari yake fita daga cikin baka, wannan itace alamar su"
Yana cikin:
صحيح البخاري - كتاب التوحيد.

Al-ƙisɗalani a sharhin wannan hadisi yake cewa:
(من قبل المشرق أي من جهة شرق المدينة كنجد وما بعدها)
(Ta ɓangaren gabashi ai ta jihhar gabashin madina - kamar najadu da bayan ta).
- Najadu shine matattaran wahabiyawa kuma tushen su na farko wanda daga nan dukka fitinar wahabiyya take fitowa...
Shi yasa malaman zamani sukace: babu buƙatan wallafa littafi domin yin raddi wa wahabiyawa, ya isa ka fito ka bayyana alamomin su, domin su kan su basaso a rinƙa bayyana alamun nasu.

5 - Yazo a hadisi dake sifanta siffofin khawarij cewa: (Suna kashe ma'abota musulunci suyi iddi'a'in cewa ma'abota bautan gumaka ne).
Ibn Taimiyya ma ya kawo a littafin sa.
- Wannan shine sifa da halin wahabiyawa, basa cinna wutar fitina da yaƙi da kisa sai akan ma'abota fuskantar alƙibla, a tarihi babu inda aka kawo tarihin cewa sun yaƙi masu bautan gumaka, kai a cikin littafinsu ma babu tunkarar masu bautan gumaka.

6 - Bukhari ya kawo daga ibn umar a siffanta Khawarijawa cewa: (Haƙiƙa su sun ɗauki wannan ayoyi da ta sauƙa akan kafirai, suka sanya ta akan muminai).
- Duba:
- صحيح البخاري - كتاب إستتابة المرتدين - باب 5)

- A wani ruwayan kuma:, yazo daga Ibn Abbas yace: (Kada ku zamto kamar Khawarijawa, sunyi tawilin ayoyin Alkur'ani akan ma'abota alƙibla, haƙiƙa wannan ayoyi ta sauƙa ne akan Ahlul-kitabi da mushrikai, suka sanya akan su (akan musulmai) suka sheƙar da jini, suka halasta dukiyar su).

Wadannan fa sune wahabiyawa, Ya Allah kayi mana tsari dasu.

24 May 2023,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...