Shaheed Mutahhari (R) ya naqalto daga Malamin sa masanin Allah wato Mirza Ali Shirazi yake cewa:
"A cikin mafarki na naga cewa gani nan na mutu, a lokacin ne naga ruhi na yabar jiki na, nan fa naga an dauke ni zuwa makabarta, bayan an kaini aka binne ni, haka suka barni ni kadai cikin kabari ina tsoro, kwatsam sai naga kare yana kokarin shigowa cikin kabari na, sai nayi tunanin wannan wani mummunan aiki ne na aikata shi ya fito min a suffar kare, haka nan na shiga damuwa, a wannan lokacin ne Sayyidush-shuhada Imam Hussein (AS) yazo min yace: Kada ka damu domin zan nisantar dashi daga gareka"
Daga littafin:
قصص من عالم الأرواح.
Shafi na 51.
Haka ke nuna Imam Hussein (AS) baya barin wanda yayi ruqo dashi anan duniya.
#السلام_عليك_يا_أبا_عبدالله.
© 17/2/2022
© Emran Darussalam
Comments
Post a Comment