Skip to main content

DAGA TASKAR MAGABATA (7)


Sayyid Ku'i (R) a wani muhadaran da ya gabatar a Hauza yake cewa: "Misali: akwai wani birni da cikin sa akwai wasu mutane dake rayuwa cikin duhu mai tsanani, matsaloli kuma suna faruwa dalilin wannan duhun da suke ciki, sarkin garin kuma ya kasance mutum ne mai hikima, sai a binciken sa ya gano fitila da zata iya haskaka garin dukkan shi, sai wannan sarki ya sanya wannan fitila domin mutane su amfana gaba daya, Haka mutane suka yi farin ciki da hakan, bayan wani ɗan lokaci sai aka samu wasu daga mutanen garin suka fasa fitilar, amma da yake shi wannan sarki yana son mutanen sa sai ya sanya wata fitilar daban, sai suka ƙara fasawa, haka ya rinka sanyawa suna fasawa har suka fasa fitilu goma sha daya, sai ya zamto fitila ɗaya tilo ta rage masa, ko yaya zayyi?
Idan ya fitar da fitila ta goma shs biyun zasu ƙara fasawa.
Hikima da hankali abinda suke cewa anan shine: Kula da wannan fitila shine yafi.
Sai wannan sarki ya boye fitilar, yaƙi fitar dashi.
Yayi hakane domin mutanen su hankalta kuma su san muhimmancin wannan fitila, ta yanda babu wani da zai ƙara yunkurin fasawa, idan wannan lokaci yayi sannan ya fidda shi.

ABIN LURA
Kamar hakane Allah maɗaukaki ya sanya mana Imamai goma sha biyu a bayan fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S), su ɗin fitilu ne masu haske dake haskaka ma mutane hanya, (su shiryar dasu) amma sai mutane suka kashe su ɗaya bayan ɗaya, wannan dalili yasa Allah madaukaki ya ɓoye na Karshen su Imam Mahdi (Atfs)  saboda son da yake wa mutane, sai su amfana da shi a yayin da suka shirya, kuma suka hankalta suka bukaci hakan, a lokacin ne duniya zata cika da zalunci sai mutane su gane cewa babu mafita sai ta hanyar wannan fitila (Imam Mahdi (Atfs), sai ya bayyana ya cika kasa da adalci, bayan ta cika da zalunci.

Ya Allah ka gaggauta bayyanar Imam Mahdi (Atfs)

09-07-2022.
© Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...