Skip to main content

DAGA TASKAR MAGABATA (7)


Sayyid Ku'i (R) a wani muhadaran da ya gabatar a Hauza yake cewa: "Misali: akwai wani birni da cikin sa akwai wasu mutane dake rayuwa cikin duhu mai tsanani, matsaloli kuma suna faruwa dalilin wannan duhun da suke ciki, sarkin garin kuma ya kasance mutum ne mai hikima, sai a binciken sa ya gano fitila da zata iya haskaka garin dukkan shi, sai wannan sarki ya sanya wannan fitila domin mutane su amfana gaba daya, Haka mutane suka yi farin ciki da hakan, bayan wani ɗan lokaci sai aka samu wasu daga mutanen garin suka fasa fitilar, amma da yake shi wannan sarki yana son mutanen sa sai ya sanya wata fitilar daban, sai suka ƙara fasawa, haka ya rinka sanyawa suna fasawa har suka fasa fitilu goma sha daya, sai ya zamto fitila ɗaya tilo ta rage masa, ko yaya zayyi?
Idan ya fitar da fitila ta goma shs biyun zasu ƙara fasawa.
Hikima da hankali abinda suke cewa anan shine: Kula da wannan fitila shine yafi.
Sai wannan sarki ya boye fitilar, yaƙi fitar dashi.
Yayi hakane domin mutanen su hankalta kuma su san muhimmancin wannan fitila, ta yanda babu wani da zai ƙara yunkurin fasawa, idan wannan lokaci yayi sannan ya fidda shi.

ABIN LURA
Kamar hakane Allah maɗaukaki ya sanya mana Imamai goma sha biyu a bayan fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S), su ɗin fitilu ne masu haske dake haskaka ma mutane hanya, (su shiryar dasu) amma sai mutane suka kashe su ɗaya bayan ɗaya, wannan dalili yasa Allah madaukaki ya ɓoye na Karshen su Imam Mahdi (Atfs)  saboda son da yake wa mutane, sai su amfana da shi a yayin da suka shirya, kuma suka hankalta suka bukaci hakan, a lokacin ne duniya zata cika da zalunci sai mutane su gane cewa babu mafita sai ta hanyar wannan fitila (Imam Mahdi (Atfs), sai ya bayyana ya cika kasa da adalci, bayan ta cika da zalunci.

Ya Allah ka gaggauta bayyanar Imam Mahdi (Atfs)

09-07-2022.
© Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan.

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan. A lokacin da Sayyid Muhammad Baƙir Sadr yake neman ilimi Ƙanwarsa Bintul Hudah tace: "Na kasance tare da ɗan'uwana a wancan lokacin muna tattara kuɗin da muke samu, koda kuwa kaɗan ne, sai Sayyid ya sayi littafi da su, mu karanta mu fahimta. Daga baya sai ya sayar da littafin domin ya sayi wani. Haka muka ci gaba da rayuwa bayan hijirarmu zuwa Najaf al-Ashraf" - Amma daga ƙarshe mai ya faru? Ilimin shi Sayyid Muhammad Baƙir Sadr (QS) da rubuce rubucen shi sun gajiyar da masu bincike, saboda duk wani mai ilimi da ya karanta littattafansa sai ya jinjina masa, ga kaɗan daga shaidan manyan Malaman Shi'a a kansa: - Ayatullah Al-ʿUzma Sayyid Abul Qasim Al-Khuʾi (QS) yace: "Lallai Najaful Ashraf tana alfahari da Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr. Lallai Allah Maɗaukaki Ya bai wa wannan Sayyid abin da bai ba wa wani ɗalibina ba." - Sayyid Ruhullah Al-Musawi Al-Khumaini (QS) yace: "Sayyid Muhammad Baqir Sadr yana daga cikin fitattun M...