Skip to main content

JAGORA ABIN KOYI SHEIKH MUHAMMAD NUR DASS (H).



Hujjatul Islam Sheikh Nur Dass (H) Malami ne na shi'a, kuma wakilin Babban Marji'i Ayatullah Sayyid Ali Khamnei (DZ) bangaren Shari'a a Najeriya, wakilcin da ba'a taɓa samun irin sa ba a kaf Nahiyar Afrika.

Yana daga cikin ƙoƙarin shi a Najeriya:
Assasa Mu'assasar RASULUL A'AZAM FOUNDATION (RAAF), wacce ta kasance mu'assasa ce ta Shi'a Zallah tare da yima wannan Mu'assasar rijista a hukuman ce, ta cika sharruɗa dukkan sharruɗa.

Rasulul A'azam Foundation (RAAF) Mu'assasa ce dake buɗe makarantun Hauzozin ilimi da markazozi dan yada addinin musulunci cikin shi'anci tsantsa, tana da Makarantun Hauzozi da Masallatai a jihohi daban daban a faɗin Nigeria, kuma duka makarantu ne masu rijista waɗanda aka gina akan tsari, kuma makarantu ne da aka yi musu ginin zamani.

Tana da keɓantaccen sashe na abinda ya shafi kira da tabligh, wannan sashe ya tara muballigai (Masu isar da sakon musulunci) da yawa a karkashin sa, duka dan Isar da sakon Ahlul-bayt (AS) a faɗin kasar ta Nigeria, Shugaban wannan sashe shine Hujjatul Islam wal muslimin Shekh Bashir lawal kano (H), wanda ake masa laqabi da Sautush~shi'a.

Haka nan wannan shugaba kuma wakilin Sayyed Ali Khamnei (DZ) ya assasa babban Hauza a birnin kano, sunan wannan Makaranta HAUZATU BAQIRUL ULUM, wanda shi ke jagorantar wannan makaranta, an samu ɗalibai dayawa wadanda suka sha madarar ilimi suka fita suma Suna taimakawa a ɓangaren tabligh yanzu haka.

Ta ɓangaren ƙoƙari da yayi a ɓangaren siyasa da janibin jama'a kuma akwai:
1. Yaɗa abinda ya shafi saƙafa da siyasa tsakanin jama'a, yayi haka ne domin farkar da ƴan shi'ar ƙasar wajen shiga cikin al'amuran da suka shafi ƙasa, kuma ayi dasu saboda suma ƴan ƙasa ne masu lasisi.

2. Wayar da kan ƴa shi'a a abinda ya shafi mahimmancin siyasa, da tsayawa takara (kamar sauran ƴan ƙasa da sauran ƙungiyoyi).

3. ƙoƙarin shi na samar da haɗin kai tsakanin ƙungiyoyin Musulunci (SHI'A DA SUNNA) da ƴan shi'a suma a junan su (bil akhas), haƙiƙa ya taka rawar gani a waɗan nan janibobin.

4. Gusar da mummunan ganin da hukuma take yiwa ƴan shi'a daga ƴan tawaye kuma masu taka doka da oda, zuwa ƴan ƙasa na gari masu kishin ƙasar su.

5. Akwai kuma ƙoƙarin shi na tarwatsa shirin wahabiyawa da suke na ƙoƙarin ɓata sunan shi'anci a cikin ƙasa, tare da sauran matakai da suka dace ta ɓangaren hukuma, kuma Alhmdlh ya samu nasara sosai a wannan yunƙuri nashi.

6. Karantar da aƙidar shi'anci yadda yake asali a musulunci, tatacce tsaftatacce daga ruwayoyin da wahabiyawa suke kawowa na ƙarya, tare da nisantar dashi daga kaucewa tsari.

6. Wannan Mu'assasa ta RASULUL A'AZAM FOUNDATION (RAAF) ta gina Masallacin Shi'a na Juma'a wanda shine farkon masallacin Shi'a a kaf Nigeria, sannan an gina shi bisa tsari da Neman izinin hukuma, wanda aka gina a Dawanau dawakin tofa dake kano Nigeria, Masallaci ne babba wanda a gefen shi aka Gina ajujuwa dan karantarwa da babban ɗakin taro wato (Hall) da banɗakai duka domin ciyar da shi'anci gaba, Akan gabatar da salloli biyar na yau da kullum a cikin sa, da sauran ibadoji da tarurrukan addini.

7. Tura adadi mai yawa na ɗalibai makarantun Hauza domin ci gaba da karatun su na addini da samun ilimi mai zurfi.

8. Ya taimaka wajen ƙarfafawa matasa da taimaka musu domin ci gaba da Karatun jami'a, kuma Alhamdulillah dayawa sun amfana da wannan abin alkairin, haka har yanxu wasu Suna amfana.

9. Yana Daga abun da yayi: kiran shi da yayita yi tsakanin hukumar Nigeria da Harkar Musulunci a Nigeria wanda Sheikh Zakzaki ke jagoranta dan zama a tattauna a gane ina Matsala take tare da magance ta ya zama daga ƙarshe an samu fahimtar juna a tsakani.

10. Bai tsaya nan ba a ɓangaren hidimtawa addini duk dare idan ka kira wayar shi zai amsa, koka tura masa sakon tex na abinda ya shafi tambaya ko neman warware wani ishkali da ya bijiro maka zai amsa maka, kodai ta hanyar message ko ta hanyar kira.

Duka kuma tare da taimakawan Sauran malaman dake tare da shi, Sheikh Saleh Muhammad Sani Zaria da Sheikh Bashir Lawal kano, da sauran Malamai a Hauza matattarar alkairai.

Fatan mu shine: Allah ya kare shi, tare da bashi ƙarfin gwiwa cikin abubuwan da yake gabatarwa, Allah ka kare su.

Jaridar Ahlulbaiti Online

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...