Skip to main content

Gareku Muballigai!

Babban Marji'i Sheikh Wahid AlKurasani (DZ) yace:

Kada ku cuɗanya maganar ɗan Adam da Maganar Allah.

Haƙiƙa wannan Aƙida tuni ne ña jinin Imam Hussain Bin Ali (AS), da ƴayan itacen zalunci da tsare Sayyida Zainab (AS) da akayi, da gadon sare hannun Abulfadlul Abbas... Wajibi ne mu san ƙimar wannan Aƙida mai girma, sannan wajibi ne mu san girman mas'uliyyarmu a kanta (ita aƙidar)

A yayin da kuke fita daga gidajenku zuwa tafiya wajen Tabligin Addinin Musulunci, damuwarku ya zamto shine kiyaye rukunan wannan Aƙida, da wannan mazhaba ta gaskiya, idan kuka ga wata zuciya da take da wilaya amma shakka ya tsiro a cikinta, to ku kawar da shakkun (da ke cikinta), idan kuma kuka ga an jefo shubuha, to ku kare ta... A yayin nan ladanku zai zamto fiye da dirhami da dinare! Zai zamto kamar yadda Amirulmu'uminin (AS) yake cewa: "Wanda ya ƙarfafa miskini a cikin addininsa, mai rauni (da'eyfi) iliminsa... Allah zai sanar da shi a yayin da ake sanya shi a cikin ƙabarinsa cewa, kace: Allah ne Ubangijina, Muhammad ne Annabina, Ali ne shugabana, Ka'aba ce alƙiblata, Alkur'ani shine farin cikina kuma alƙawarina, Muminai ne ƴan uwa na, Sai Allah yace: haƙiƙa ka zo da hujja, don haka na baka mafificin Aljanna, a yayin ne za'a canza masa ƙabarinsa zuwa raudan Aljanna, daga mafificin raudodinta. (Al'ihtijaj Juz'i na 1 Shafi na 10).

Allah ya yi masa talƙinin kalmar da baya tasawwurin wacce ta fita, wannan kuwa alƙawarin Amirulmu'uminin ne gareku, idan (ku) kuka ƙarfafi aƙida mai rauni domin sanin addininsa, kuka tabbatar da zuciyarsa a kan mazhabi na gaskiya, (zai zamto) farkon tasirin aikin ku a cikin ƙabari shine talƙinin da Allah madaukaki zai yi muku! Sannan tasirin za kai ga ƙabarinsa ya zamto rauda daga raudodin Aljanna.

Haƙiƙa lada ne da ya wuce tsammaninmu, kuma ya fi ƙarfin tasawwurinmu! Ku sanya dukkan ƙoƙarinku a cikin wannan tunani wajen yaɗa girman Ahlulbaiti (AS), kuma nufin ku da hadafinku ya zamto shine yiwa mutane bayanin Alƙur'ani da Sunna kaɗai, kada ku karkata daga wannan khaɗɗin, kuma ku sani! Hanyar yin tasiri a zukatan mutane ya taƙaitu ne da Alƙur'ani da hadisan Itran Annabi (S), hanyar da ba wannan ba kuskure ce! Kada ku cuɗanya maganar ɗan Adam da Maganar Allah, kada ku gwada ƙasa da sama, ko ku yi ƙoƙarin gwada wahami da haƙiƙa.

07/05/2024,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

AYYUKAN DAREN FARKO NA WATAN RAJAB

Ayyukan daren farko na watan Rajab: 1– Wanka (Gusl): An rawaito daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Duk wanda ya samu watan Rajab, ya yi wanka a farkonsa, tsakiyarsa da ƙarshensa, zai fita daga zunubansa kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi.” 2– Raya daren (ibada a daren): Wannan na daga cikin darare huɗu da ake ƙarfafa mustahabbancin rayar da su. An rawaito daga Abu Abdullahi (AS), daga mahaifinsa, daga kakansa, daga Ali (AS) cewa ya ce: “Yana so ya keɓe kansa a darare huɗu cikin shekara: daren farko na Rajab, daren tsakiyar Sha’aban, daren Idin Fitr, da daren Idin layya.” 3– Addu’a lokacin ganin jinjirin wata: اللّهُمَّ أَهِلَّهُ عَلّيْنا بالأمْنِ وَالإيْمانِ وَالسَّلامَةِ وَالإسْلامِ رَبِّي وَرَبُّكَ الله عَزَّ وَجَلَّ. Kuma Manzon Allah (SAW) idan ya ga jinjirin Rajab yana cewa: اللّهُمَّ بارِكْ لَنا فِي رَجَبٍ وَشَعْبانَ وَبَلِّغْنا شَهْرَ رَمَضانَ وَأَعِنَّا عَلى الصِيامِ وَالقِيامِ وَحِفْظِ اللّسانِ وَغَضِّ البَصَرِ وَلا تَجْعَلْ حَظَّنا مِنْهُ الجُوعَ وَالعَطَشَ. Sal...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...