Skip to main content

Gareku Muballigai!

Babban Marji'i Sheikh Wahid AlKurasani (DZ) yace:

Kada ku cuɗanya maganar ɗan Adam da Maganar Allah.

Haƙiƙa wannan Aƙida tuni ne ña jinin Imam Hussain Bin Ali (AS), da ƴayan itacen zalunci da tsare Sayyida Zainab (AS) da akayi, da gadon sare hannun Abulfadlul Abbas... Wajibi ne mu san ƙimar wannan Aƙida mai girma, sannan wajibi ne mu san girman mas'uliyyarmu a kanta (ita aƙidar)

A yayin da kuke fita daga gidajenku zuwa tafiya wajen Tabligin Addinin Musulunci, damuwarku ya zamto shine kiyaye rukunan wannan Aƙida, da wannan mazhaba ta gaskiya, idan kuka ga wata zuciya da take da wilaya amma shakka ya tsiro a cikinta, to ku kawar da shakkun (da ke cikinta), idan kuma kuka ga an jefo shubuha, to ku kare ta... A yayin nan ladanku zai zamto fiye da dirhami da dinare! Zai zamto kamar yadda Amirulmu'uminin (AS) yake cewa: "Wanda ya ƙarfafa miskini a cikin addininsa, mai rauni (da'eyfi) iliminsa... Allah zai sanar da shi a yayin da ake sanya shi a cikin ƙabarinsa cewa, kace: Allah ne Ubangijina, Muhammad ne Annabina, Ali ne shugabana, Ka'aba ce alƙiblata, Alkur'ani shine farin cikina kuma alƙawarina, Muminai ne ƴan uwa na, Sai Allah yace: haƙiƙa ka zo da hujja, don haka na baka mafificin Aljanna, a yayin ne za'a canza masa ƙabarinsa zuwa raudan Aljanna, daga mafificin raudodinta. (Al'ihtijaj Juz'i na 1 Shafi na 10).

Allah ya yi masa talƙinin kalmar da baya tasawwurin wacce ta fita, wannan kuwa alƙawarin Amirulmu'uminin ne gareku, idan (ku) kuka ƙarfafi aƙida mai rauni domin sanin addininsa, kuka tabbatar da zuciyarsa a kan mazhabi na gaskiya, (zai zamto) farkon tasirin aikin ku a cikin ƙabari shine talƙinin da Allah madaukaki zai yi muku! Sannan tasirin za kai ga ƙabarinsa ya zamto rauda daga raudodin Aljanna.

Haƙiƙa lada ne da ya wuce tsammaninmu, kuma ya fi ƙarfin tasawwurinmu! Ku sanya dukkan ƙoƙarinku a cikin wannan tunani wajen yaɗa girman Ahlulbaiti (AS), kuma nufin ku da hadafinku ya zamto shine yiwa mutane bayanin Alƙur'ani da Sunna kaɗai, kada ku karkata daga wannan khaɗɗin, kuma ku sani! Hanyar yin tasiri a zukatan mutane ya taƙaitu ne da Alƙur'ani da hadisan Itran Annabi (S), hanyar da ba wannan ba kuskure ce! Kada ku cuɗanya maganar ɗan Adam da Maganar Allah, kada ku gwada ƙasa da sama, ko ku yi ƙoƙarin gwada wahami da haƙiƙa.

07/05/2024,
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...