Skip to main content

Labari Mafi Ƙayatarwa A Ranar Gadir.



Hassan ya kasance ɗan shi'a kuma dalibi a makarantar da mafi yawan ɗaliban ta Ahlussunnah ne.
Wata rana malami zai fita daga aji sai yace:
Ya kai Hassan taso ka zauna a gurin zama na, kada ka yarda da wani rikici ko suruce-suruce a tsakanin ɗalibai har zuwa dawowa na!.
Sannan yayi musu umurni akan suyiwa Hassan ɗa'a kuma suyi masa biyayya!
A nan ne Hassan ya tashi tsaye sai yacewa Malamin:
Shin zai iya yiwuwa inyi tambaya?
Malami yacewa Hassan Bismillah, zaka iya tambayar ka!
Sai Hassan yace: Kunce Annabi (S) yabar duniya ba tare da ya ayyana kalifa a bayansa ba, shin Annabi (S) bai kai malaman mu (Masu girma) ilimi da tsantseni da sanin ya kamata bane? Tunda kunce bai ayyana wanda zaici gaba da tafiyantar da al'amuran addini a bayan sa ba, kuma bai sanya wanda zai ci gaba da hana rikici tsakanin al'ummar musulmi da daular ubangiji a bayansa ba?!! 
Dukda cewa malam kasan zaka dawo anjima amma ka daura ni a matsayin kalifa a bayan ka, to taya Annabi (S) da yasan idan ya bar duniya bazai dawo ba yabar al'ummar musulmi haka nan kara zube ba kalifa?
Nan wannan Malamin yayi shiru na ɗan wani lokaci, yana ta tunanin hanyar da zai ɓullo wa Hassan, da yaga bashi da amsar da zai bashi sai ya waske ta hanyar tura Hassan wajen shugaban makaranta domin a azabtar da shi!!!
Bayan an kai Hassan wajen shugaban makaranta sai ya bukaci Hassan ya tafi gida domin ya taho da majiɓancin lamarin shi,
Washe gari sai ga Hassan yazo tare da abokin shi na makaranta,
Nan shugaban makaranta yayi mamaki, yace: Hassan me yasa baka taho da majibancin lamarin ka ba?
Sai Hassan yace: Wannan shine Majiɓancin lamari na.
Sai shugaban makaranta ya fusata, yace: Ina nufin Majibancin lamarin ka, ma'ana wanda yake da wilaya akan ka, kamar mahaifin ka...
A nanne Hassan yace: A yanzu kace: Majiɓancin lamari shine wanda yake da wilaya akai na, kamar mahaifin na...
Amma a lokacin da Annabi Muhammad (S) yace: "Shin ba nine mafifici akan muminai daga kawunan ku ba? Sai sahabbai suka ce haƙiƙa hakane, sai yace: wanda duk na zamo shugaba a gare shi, ya riƙi wannan Alin a matsayin shugaba a gare shi,
Sai ku kuma kuka ce: Ai (maula) Annabi (S) yana nufin Abota ne, da kyakkyawan alaqar dake tsakanin shi da Ali, shin ba haka bane?
Wannan tasa yanzu nazo muku da abokina wanda nake son shi, kuma muke da kyakkyawan alaka da shi, to meyasa ba zaku karɓe shi a matsayin Majibancin lamari na ba?
Nan fa shugaban makaranta yayi shuru, domin bai san amsar da zai bawa Hassan ba!

Akwai Darasi Ga Masu Hankali!

Ya Allah ka sanya mu daga cikin masu wulaya wa AHLULBAITI (AS) ka kyautata makomar mu.

✍️ Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...