Skip to main content

🌑 Daren Bankwana – Tare Da Ummul Masa'ib Sayyida Zainab (AS).

🌑 Daren Bankwana – Tare Da Ummul Masa'ib Sayyida Zainab (AS).

A daren goma ga watan Muharram – Daren Bankwana, ranar kafin yaƙin Karbala – Su Sayyida Zainab sun cika da baƙin ciki, da jiran irin ƙaddarar da zata faru. Wannan dare shi ne lokacin da Sayyida Zainab (عليها السلام) ta fuskanci mafificin nauyin rayuwa, da azaba da jimami.á

Shine dare na karshe da zata ga fuskar manyan ‘yan uwanta,

Dare ne da ke ƙunshe da ƙunci da baƙin ciki da rabuwa da ƙaunar da babu kamarsa.

💔 Aƙila Zainab da Imam Husain (AS): Bankwana Na Ƙarshe

A cikin duhun dare, Sayyida Zainab ta tunkari ɗan uwanta Imam Husain tana kuka, zuciyarta cike da firgici da damuwa tace:

"Yā Aba Abdillah... shin wannan shi ne bankwana na karshe?
Shin daga gobe zan zama cikin kaɗaici ba tare da kai ba?
Shin daga gobe zanci gaba da ɗaukan yaran da suka rasa iyayensu (marayu)?

Imam Husain (عليه السلام) ya rungume ta da ƙauna, yana cewa:

"Kiyi haƙuri ya Zainab… akwai babban jarabawa a gobe, amma nasara tana tare da juriya da tawakkali. Kin kasance abin alfahari ga Ahlulbayt, kici gaba da kasancewa a hakan."

🔥 Lokacin da zuciya ke kuka

Wannan dare ba kawai dare ne na jimami da kuka ba, amma dare ne da Sayyida Zainab ta ji kamar zuciyarta za ta fashe, saboda yadda musibu suka taru sukai mata yawa.

Tana ganin:
Yara wasu daga ƙananan yara suna barci cikin ɗaci, ba tare da sanin cewa gobe za su zama marayu ba, wasu kuna suna ta kiran ƙishirwa! ƙishirwa!! ƙishirwa!!!

Kamar su Ruqayya, da Ali Asghar, da Sakina...

Jaruman Ahlulbayt da Sahabban Imam Hussain (AS) suna shirin fuskantar shahada, amma ba a san su da fargaba ba, sai tawakkali, da jin yaƙinin zasuyi nasara.

🕯️ Sayyida Zainab: Tutar Karfafa Imani

Daren Bankwana ya tabbatar da cewa Sayyida Zainab ba mace ce kamar sauran mata gama gari ba — ita tutar karfafa ce, uwar karimci, madubin juriya da jarumta.
Ta ƙaddara tun kafin hasken safiya ya fito, cewa:

"Duk da wutar kaddara, ba zan bar tutar Husain (ع) ta faɗi ba!"

🌌 Wani Zubi Na Zuciya, Ta Kasance A Irin Wannan Dare Na Goma Tana Waƙe Tana Cewa:

Ya dare, kada ka ƙare da wuri...
Ka bar ni in ƙara kallon fuskar ɗan uwana,
Ka bar ni in rungumi Ali Asghar rumguma na ƙarshe,
Ka bar ni in sumbaci Raƙayya kafin safiya ta iso.
Ka bar ni in yi kuka da gwiwata akan ƙasa...
Domin gobe, bansani ba ko zan sami damar hakan..."

Ya dare… ka tsawaita!
Na rasa Abbas,
Na rasa Ali Akbar, tauraron fata,
Na rasa yara da suke dariya yau, gobe kuma su zama abin kuka.

Na kalli Ruqayya tana barci a ƙurya,
Na sumbaci kumatun Ali Asghar,
Ina jin numfashinsu, amma zuciyata tana ɓari —
Domin ban san ko zan sake jin hakan bayan gobe ba.

Ya dare... ka zamo shaida!
Husain yana ibada, yana salla,
Yana addu'a ga Allah da hawaye a fuskarsa,
Amma zuciyarsa cike take da tawakkali da yarda.

Na tunkare shi…
Na kalli ɗan uwana wanda na tashi da shi,
Na ce masa: "Waye zai zama jinina bayan kai?"
Sai ya ce da ni:

 "Zainab! Ke ce amana, ke ce mai ɗaukar tutar juriya.
Ki zama kamar bango ga waɗanda suka rage!" 
Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un...

Ya dare… ba zan manta da kai ba.
Ka shaida cewa karfin mata ba ya karewa,
Ka shaida cewa Zainab ta dora nauyin Ahlulbayt a kafaɗarta.
Ka shaida cewa, da safe, duniya za ta canza…
Amma sunan Husain zai rayu har abada!

Haka ɓangarensu Imam Hussain (AS) suka ci gaba da shiri, daga masu sallan bankwana, sai masu tasbihi da istigfari da salatin Annabi fuskantarsu hawaye na kwaranya.

Ɗaya ɓangaren na maƙiyawa kuma suna ta shewa, suna ihu, suna buga ganga, suna ta ciye-ciye da shaye shaye da shirin sheƙar da jinin Ahlulbaiti a gobe Ashura (Goma Ga Watan Almuharram). Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un

Sat, Jul 5,
2025.
Emran Darussalam.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan.

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan. A lokacin da Sayyid Muhammad Baƙir Sadr yake neman ilimi Ƙanwarsa Bintul Hudah tace: "Na kasance tare da ɗan'uwana a wancan lokacin muna tattara kuɗin da muke samu, koda kuwa kaɗan ne, sai Sayyid ya sayi littafi da su, mu karanta mu fahimta. Daga baya sai ya sayar da littafin domin ya sayi wani. Haka muka ci gaba da rayuwa bayan hijirarmu zuwa Najaf al-Ashraf" - Amma daga ƙarshe mai ya faru? Ilimin shi Sayyid Muhammad Baƙir Sadr (QS) da rubuce rubucen shi sun gajiyar da masu bincike, saboda duk wani mai ilimi da ya karanta littattafansa sai ya jinjina masa, ga kaɗan daga shaidan manyan Malaman Shi'a a kansa: - Ayatullah Al-ʿUzma Sayyid Abul Qasim Al-Khuʾi (QS) yace: "Lallai Najaful Ashraf tana alfahari da Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr. Lallai Allah Maɗaukaki Ya bai wa wannan Sayyid abin da bai ba wa wani ɗalibina ba." - Sayyid Ruhullah Al-Musawi Al-Khumaini (QS) yace: "Sayyid Muhammad Baqir Sadr yana daga cikin fitattun M...