Skip to main content

Posts

Showing posts from June, 2026

Ina Ɗaliban Ilimi???

Ina Ɗaliban Ilimi??? Sheikh Muhammad Taƙi Bahjah (QS) yace: Ta hanyar ƙwarewa, ya zama abu sananne gare ni cewa: "idan ba'a sami sakaci a cikin lamuran ibada ba, to za a iya kammala darasin da ke bukatar yin awa ɗaya cikin mintuna goma! (tare da fahimta)"  Allah yana cewa: "Kuma kuji tsoron Allah da takawa, sai Allah Ya sanar da ku" – Baqarah, aya 282. Sharhi: Wato a yayin da bawa ya kula da janibin ibada tare da tsoron Allah, zai sami saurin fahimta a janibin karatu, zai fahimci karatu cikin ƙanƙanin lokaci ba tare da shan wahala ba. 05/06/2024, Emran Darussalam

🌹✨ RANAR JADDADA MUBAYA'A DA ABOTA – RANAR GHADIR ✨🌹

🌹✨ RANAR JADDADA MUBAYA'A DA ABOTA – RANAR GHADIR ✨🌹 💚 Ɗan uwa zo Mu Sake Jaddada Abota da Ƴan'uwantaka Kan Wilayar Amirul Muminina Imam Ali (A.S.) 💚 🤝📜 Ni Emran Darussalam Ina cewa gare ka: "Na ƙaunace ka saboda Allah, na yi abota da kai saboda Allah, kuma na yi alkawari da Allah, Mala'ikunsa, Littattafansa, Manzanninsa da Imamai Ma'asumai (A.S.) cewa idan na kasance daga cikin mutanen Aljanna kuma aka ba ni izinin shiga Aljanna, ba zan shiga ba sai tare da kai." 💐 Ɗan uwa ka amsa da: ✨ "Na karɓa." ✨ 🤲 Sannan: "Na yafe maka dukkan haƙƙoƙin 'yan'uwantaka da ke tsakanina da kai, sai dai tabbatuwa a kan Wilayar Amirul Muminina Imam Ali (A.S.) da sauran Ahlulbaitin Tsira (A.S.), da kuma haƙƙin shafa'a, addu'a da ziyara." 💚❓ _Shin ka karɓa?_ ❓💚 🌺 Wannan wata kyakkyawar al'ada ce ta ranar Eidul Ghadir, wadda ke ƙarfafa zumunci, soyayya da haɗin kai saboda Allah. A wannan rana, mabiya Ahlulbaiti (A.S.) suna sabunta ...

Tarbiyya A Wajen Malaman Shi’a, Musamman A Mahangar Falsafar Tarbiyya Da Akhlāq A Fikirar Ahlul Bayt (a.s).

Tarbiyya A Wajen Malaman Shi’a, Musamman A Mahangar Falsafar Tarbiyya Da Akhlāq A Fikirar Ahlul Bayt (a.s). Tarbiyya tana nufin tsari na ilmantarwa da gina ɗan adam don isa zuwa ga kamala (Samun yardan Allah ) – wato kai mutum zuwa matakin da Allah Yake so, ta hanyar gyara Aƙida, ladubba, da halaye, da kuma shiryar da zuciya zuwa ga Ubangiji (Mahalicci). 🔹 Ma’anar “Tarbiyya” A Harshen Shi’a: Kalmar "Tarbiyya" tana nufin: "Nuna kulawa da gina mutum daga matakin ƙanƙanta zuwa manyanta, tare da ci gaba da tsare shi a kowane mataki na ci gaba – har ya kai ga kamala (Samun yardan Allah). Saboda haka, tarbiyya a mahangar Shi'a ba kawai koyar da ilimi ba ce, amma gyaran ruhi ne, halayya, da tunani, bisa koyarwar Qur’ani da Ahlul Bayt (a.s). Mahimmancin Tarbiyya A Makarantar Ahlul Bayt (a.s): 1. Tarbiyyar Imani: Tarbiyyantar da mutum a kan gaskata da kaɗaita Allah (tawhīd), Ma’ad (Makoma ƙiyama), Annabta, da Imama. Wannan shi ne tushen tarbiyya. 2. Tarbiyyar Akhlaqi (Halaye...