Skip to main content

GIRMAMAWAN MUSULUNCI GA MACE.


- Addinin musulunci ya tausayawa Mace yayin da ya sauƙe ciyarwan  ƴayan ta da mijin ta da iyayen ta daga kanta, hatta ciyar da kanta bai daura mata ba, ya wajabtawa iyayen ta ne a yayin da take tare dasu, ya ɗaurawa mijin ta a yayin da tayi aure.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya wajibcin bata cikakken sadaki, bai wajabta mata bada ko sisi ga miji ba.

- Ya tausayawa mace a yayin da yace wa ɗa, "Mahaifiyar ka! Mahaifiyar ka!! Mahaifiyar ka!!! Sannan mahaifin ka", duka don girmamawa gare ta.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sauƙe mata farillan hajji muddin bata tare da mijin ta ko wani muharrami da zai tsare ta har zuwa dawowan ta.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya bata gadon mijin ta, dana ƴan uwan ta, dana ƴayan ta, da na iyayen ta, duk kuwa da cewa babu nauyin ciyarwan kowa a kanta.

- Musulunci ya tausayawa mace tare da girmamawa gareta a yayin da ya haramta ingancin auren ta babu waliyyi da shaidu, duka saboda kada a zarge ta ko a zubar mata da mutunci da bata silsilan ƴayan ta.

- Musulunci ya tausayawa mace tare da girmamawa gareta a yayin da wajabta bulala tamanin (a bainar jama'a) ga wanda yayi mata ƙazafi, sannan shaidar sa ba karɓaɓɓiya bace daga wannan rana.

- Musulunci ya tausayawa mace tare da girmamawa gareta a yayin da ya sanya wanda ya mutu wajen kare mutuncin ta shahidi.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya hatta bayan mutuwan ta babu mai mata wanka sai mijin ta ko makusanta gareta.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya likafanin ta fiye da na namiji, za'ayi mata sutura da likafani yanki biyar, duka saboda suturce alfarman ta.

Aminci da rahama da albarka su tabbata ga wanda ya karanta ya yaɗa shi domin amfanar wasun mu, da yaye wahamin dake zukatan masu ganin Allah ya kaskanta mace.

3rd November 2022.
© E m r a n   D a r u s s a l a m.

Comments

Popular posts from this blog

Muhimmancin Ranar Arfa A Imamiyya.

Da Alƙalamin Sheikh Imrana Darussalam  Azumin Arfa (ranar 9 ga Zul-Hijja) yana da matsayi mai girma a tsarin ibada na Imamiyya (Shi'a), kodayake yana da bambanci kadan da fahimtar Ahlus-Sunna. A mad'hab din Imamiyya, wannan rana tana da daraja ta musamman saboda kasancewarta rana mai tsarki, rana ta addu'a da tuba, kuma rana ce da Allah ke gafartawa bayinsa da dama, musamman ga wadanda ke Arafat da kuma wadanda ba su je Hajji ba. 1. Muhimmancin ranar Arfa a Imamiyya Ranar Arfa ita ce rana ta biyu mafi falala a cikin shekara bayan Laylatul Qadr. Shi’a Imamiyya suna ganin cewa wannan rana ita ce ranar kusanci da Allah, inda ana karanta addu'o'i da yawa, musamman Addu'ar Imamu Husain (a.s) a ranar Arfa da kuma Addu’ar Imam Zainul Abidin (a.s), wadanda suka kunshi falsafa mai zurfi da ruhaniya mai karfi. 2. Azumi a ranar Arfa a Imamiyya Azumin ranar Arfa yana da falala mai girma ga wanda ba ya aikin Hajji, kamar yadda ya zo a hadisan Ahlul Bayt (a.s). Ha...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Azumin Ashura Da Tasu'a... Halasci Ko Haramci?

🟥 Haramcin Azumin Ashura Da Tasu’a. 🛑 Matsaya: A mafi yawan ra’ayoyin malamai da ruwayoyin Ahlul Bayt (a.s), azumin ranar Ashura da Tasu’a yana da laifi ko haramci idan: 1. An yi shi da niyyar murna ko farin ciki da abubuwan da suka faru a Karbala. 2. An dauke shi ibada mafi girma ko kamar na Ramadan. 3. An yi shi da nufin koyi da Yazidawa da masu murnar kisan Imam Husain (a.s). 📌 DALILAI NA HARAMCI: 1. 🔥 Dalili na Tarihi: Bayan shahadar Imam Husain (a.s) a ranar Ashura (10 ga Muharram), Gwamnatin Banu Umayyah, musamman Yazid da magoya bayansa, suka mayar da ranar murnar nasara da bukukuwa. An ruwaito cewa: > "Yazid ya bada umarni a dauki wannan rana a matsayin ranar farin ciki da yin ado." Azumin Ashura da ci da sha na musamman (alwala ta musamman, girki, da cin abinci mai dadi) sun samo asali ne daga wannan ƙirƙirar da nufin wanke laifin kisan Husain (a.s). 2. 📚 Dalili daga Riwayoyin Ahlul Bayt (a.s): 📖 Imam Ja’far al-Sadiq (a.s) ya ce: > "Wannan rana (Ashu...