Skip to main content

GIRMAMAWAN MUSULUNCI GA MACE.


- Addinin musulunci ya tausayawa Mace yayin da ya sauƙe ciyarwan  ƴayan ta da mijin ta da iyayen ta daga kanta, hatta ciyar da kanta bai daura mata ba, ya wajabtawa iyayen ta ne a yayin da take tare dasu, ya ɗaurawa mijin ta a yayin da tayi aure.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya wajibcin bata cikakken sadaki, bai wajabta mata bada ko sisi ga miji ba.

- Ya tausayawa mace a yayin da yace wa ɗa, "Mahaifiyar ka! Mahaifiyar ka!! Mahaifiyar ka!!! Sannan mahaifin ka", duka don girmamawa gare ta.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sauƙe mata farillan hajji muddin bata tare da mijin ta ko wani muharrami da zai tsare ta har zuwa dawowan ta.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya bata gadon mijin ta, dana ƴan uwan ta, dana ƴayan ta, da na iyayen ta, duk kuwa da cewa babu nauyin ciyarwan kowa a kanta.

- Musulunci ya tausayawa mace tare da girmamawa gareta a yayin da ya haramta ingancin auren ta babu waliyyi da shaidu, duka saboda kada a zarge ta ko a zubar mata da mutunci da bata silsilan ƴayan ta.

- Musulunci ya tausayawa mace tare da girmamawa gareta a yayin da wajabta bulala tamanin (a bainar jama'a) ga wanda yayi mata ƙazafi, sannan shaidar sa ba karɓaɓɓiya bace daga wannan rana.

- Musulunci ya tausayawa mace tare da girmamawa gareta a yayin da ya sanya wanda ya mutu wajen kare mutuncin ta shahidi.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya hatta bayan mutuwan ta babu mai mata wanka sai mijin ta ko makusanta gareta.

- Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya likafanin ta fiye da na namiji, za'ayi mata sutura da likafani yanki biyar, duka saboda suturce alfarman ta.

Aminci da rahama da albarka su tabbata ga wanda ya karanta ya yaɗa shi domin amfanar wasun mu, da yaye wahamin dake zukatan masu ganin Allah ya kaskanta mace.

3rd November 2022.
© E m r a n   D a r u s s a l a m.

Comments

Popular posts from this blog

Daren Nisfu Sha’aban

Daren Nisfu Sha’aban Mai girma da ɗaukaka yana cewa: (Ku yi gaggawa zuwa ga gafarar Ubangijinku da Aljanna wacce fādinta ya kai sammai da ƙasa, wacce aka tanadar wa masu tsoron Allah) Aali Imran: 133. Sheikh Ṣaduq ya rawaito da ingantaccen isnadi daga Hariz as-Sijistani daga Zurara bin A‘yun, ya ce: Na tambayi Abu Ja‘afar (A.S) cewa: Me zaka ce game da daren Nisfu Sha’aban? Sai ya ce: “Allah Maɗaukaki yana gafarta wa halittunsa a wannan daren fiye da adadin gashin awakin ƙabilar Kalbiy, kuma Allah Maɗaukaki yana saukar da mala’ikunSa zuwa saman duniya da kuma ƙasa a Makka.” Kuma an rawaito da isnadi mai inganci daga Hasan bin Faḍḍal, ya ce: Na tambayi Ali bin Musa ar-Riḍa (A.S) game da daren nisfu Sha’aban, sai ya ce: “Dare ne da Allah ke ‘yantar da wuyoyi daga wuta, kuma Yana gafarta manyan zunubai.” Sannan ya ce: “Ku yawaita ambaton Allah Maɗaukaki, da neman gafara da yin addu’a a cikinsa, domin mahaifina (A.S) yana cewa: Addu’a a wannan daren karɓaɓɓiya ce.” Kuma an rawaito daga al-...

UWA TA GARI...

Uwa Ta Gari Da Alƙalamin Sheikh Imrana Haruna Darussalam  Uwa ta gari itace wacce ta tanadi waɗannan abubuwa kafin tayi aure: 1. Ilimi da Fahimta > Imam Ali (a.s) yace: "العلمُ ميراثُ الأنبياء، والمالُ ميراثُ الفراعنة." al-Kāfī, j.1, bāb fadl al-ʿilm  Ma’ana: Ilimi gadon annabawa ne, dukiya kuwa gadon masu zalunci. Wannan yana nuna cewa mace ta gari na buƙatar ilimi don tarbiyyar ƴayanta, domin kuwa itace Malama ta farko da ke fara bada ilimi a yaro tun a tsumman goyo kafin a kaiga kaishi makaranta. 2. Ƙauna da Tausayi > Imam al-Sadiq (a.s) yace: "رحم الله عبداً أعان ولده على برّه." al-Kāfī, j.6, bāb birr al-wālidayn  Ma’ana: Allah ya ji ƙan bawan da ya taimaka wa ɗansa wajen yi masa biyayya (ta hanyar ƙauna da kulawa).  Uwa ta gari tana cika gida da ƙauna da tausayi, a yayin da uwa ta haɗe wadannan abubuwa biyu to zaka samu ɗanta ya taso da tausayin al'umma da son mutane, hakan zaisa ya zamto abin so wajen mutane. 3. Tarbiyya Mai Kyau Imam Ali...

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan.

Ɗalibin Ilimi Ga Abin Koyi Nan. A lokacin da Sayyid Muhammad Baƙir Sadr yake neman ilimi Ƙanwarsa Bintul Hudah tace: "Na kasance tare da ɗan'uwana a wancan lokacin muna tattara kuɗin da muke samu, koda kuwa kaɗan ne, sai Sayyid ya sayi littafi da su, mu karanta mu fahimta. Daga baya sai ya sayar da littafin domin ya sayi wani. Haka muka ci gaba da rayuwa bayan hijirarmu zuwa Najaf al-Ashraf" - Amma daga ƙarshe mai ya faru? Ilimin shi Sayyid Muhammad Baƙir Sadr (QS) da rubuce rubucen shi sun gajiyar da masu bincike, saboda duk wani mai ilimi da ya karanta littattafansa sai ya jinjina masa, ga kaɗan daga shaidan manyan Malaman Shi'a a kansa: - Ayatullah Al-ʿUzma Sayyid Abul Qasim Al-Khuʾi (QS) yace: "Lallai Najaful Ashraf tana alfahari da Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr. Lallai Allah Maɗaukaki Ya bai wa wannan Sayyid abin da bai ba wa wani ɗalibina ba." - Sayyid Ruhullah Al-Musawi Al-Khumaini (QS) yace: "Sayyid Muhammad Baqir Sadr yana daga cikin fitattun M...