Skip to main content

Posts

Karatun Alkur'ani.

A duk sanda zuciyarku taji tana kewar ganin Imamul-Hujjah (Atfs) to ku dubi shafukan Alkur'ani... Sheikh Muhammad Taƙi Bahja (QS). Imam al-Sadiq (as) ya ce: “Al-Qur’ani alkawarin Allah ne ga halittunsa, don haka ya kamata Musulmi ya duba cikin wannan alkawari, kuma ya karanta daga cikinsa kowace rana ayoyi hamsin (50) (alal aƙall)... Alkafi Juz'i na 2, Shafi na 609. Imam Ali (AS) Yace: “Ku koyi karatun Al-Qur’ani, domin shi ne mafi kyawun zance. Ku zurfafa ilimi a cikinsa... Ku nemi warkarwa da haskensa, domin shi ne warakar zukata, Kuma ku kyautata karanta shi, domin shi ne mafi amfanin labarai.” 📚 Nahjul Balagha, Hikima ta 110. Ya Allah Ka Bamu Ikon Karanta Littafinka A Koda Yaushe. Mon, Jul 28 2025, Emran Darussalam.
Recent posts

Halin Ƙunci Da Tashin Hankali Da Al-ummar Gaza Ke Ciki.

Halin Ƙunci Da Tashin Hankali Da Al-ummar Gaza Ke Ciki. Al-ummar Gaza na fuskantar wani mummunan hali na yunwa da tashin hankali, sakamakon hare-haren da HKI ke kaiwa ba kakkautawa tun watanni da suka gabata. Yara da mata da tsofaffi na mutuwa kowace rana saboda yunwa, rashin magunguna, da rushewar cibiyoyin lafiya da rashin abinci. An kulle hanyoyin shigar kayan agaji gaba ɗaya, lamarin da ya jefa al’ummar cikin mummunan hali. Duk da wannan bala’i mai tsanani, yawancin ƙasashen Larabawa na kallon abin yana faruwa ba tare da matakin taimako mai ma’ana ba. Wasu daga cikinsu ma suna toshe hanyoyin agaji, yayin da wasu ke nuna shiru tamkar ba su da alhakin addini ko na ɗan Adam. Wannan ya jefa al’umma cikin ƙunci, tare da nuna gazawar haɗin kan Larabawa da kuma ƙarancin damuwa da rayukan ‘yan’uwa musulmi a Gaza. Halin Gaza darasi ne ga duniya baki ɗaya: ko da akwai 'yan'uwa a addini da harshe, sai an sami mutanen da ke da haƙiƙanin damuwa da shiri don taimakawa, in ba ...

HATSARIN DAKE CIKIN KETA ALFARMAR MARJI'IYYA.

HATSARIN DAKE CIKIN KETA ALFARMAR MARJI'IYYA. Sayyid Muhammad Sadiq Rowhani (DZ) yace: " ya kamata ƴayan mu maza da mata su sani cewa: cin zarafin Manyan Marji'ai "Daga ko waye hakan ya fito" alama ce ta taɓewa, ko ince girman kai da bin soye-soyen zuciya, sannan ɗaukan bashi ne a wajen Allah maɗaukaki, kuma mun sani cewa: duk wani mai wuce gona da iri akan Marji'iyya (mai albarka) wannan alama ce ta farkon faɗawa hawuya da kaucewa daga hanya, muminai ku kiyaye faɗawa cikin wannan sashe da bazaku iya tsayawa akan ƙafafun ku ba ranar kiyama. Ya Allah ka tsare mu. 24/07/2022 © E m r a n D a r u s s a l a m.

🌑 Daren Bankwana – Tare Da Ummul Masa'ib Sayyida Zainab (AS).

🌑 Daren Bankwana – Tare Da Ummul Masa'ib Sayyida Zainab (AS). A daren goma ga watan Muharram – Daren Bankwana, ranar kafin yaƙin Karbala – Su Sayyida Zainab sun cika da baƙin ciki, da jiran irin ƙaddarar da zata faru. Wannan dare shi ne lokacin da Sayyida Zainab (عليها السلام) ta fuskanci mafificin nauyin rayuwa, da azaba da jimami.á Shine dare na karshe da zata ga fuskar manyan ‘yan uwanta, Dare ne da ke ƙunshe da ƙunci da baƙin ciki da rabuwa da ƙaunar da babu kamarsa. 💔 Aƙila Zainab da Imam Husain (AS): Bankwana Na Ƙarshe A cikin duhun dare, Sayyida Zainab ta tunkari ɗan uwanta Imam Husain tana kuka, zuciyarta cike da firgici da damuwa tace: "Yā Aba Abdillah... shin wannan shi ne bankwana na karshe? Shin daga gobe zan zama cikin kaɗaici ba tare da kai ba? Shin daga gobe zanci gaba da ɗaukan yaran da suka rasa iyayensu (marayu)? Imam Husain (عليه السلام) ya rungume ta da ƙauna, yana cewa: "Kiyi haƙuri ya Zainab… akwai babban jarabawa a gobe, amma nasara tana tare da j...

Sayyida Zainab (AS) Jarumar Karbala.

Sayyida Zainab (AS) Jarumar Karbala. Gudummawar Sayyida Zainab (AS) a Karbala na daga cikin manyan shahararrun al'amura da suka bayyana matsayin mata a jihadin addini da kare gaskiya. Ta taka rawar gani a bangarori da dama kafin, yayin, da bayan yaƙin Karbala. Ga bayani a takaitace kamar haka: 1. Goyon Bayan Imam Husain (AS): Sayyida Zainab (AS) ta kasance amintacciya kuma mai sadaukarwa ga Imam Husain (AS), dan'uwanta kuma Imami a lokacin. Tana tare da shi a tafiyarsa daga Madina zuwa Makka, har zuwa Karbala. Ta kasance mai fahimta da yakinin cewa tafiyar da suke yi tafiya ce ta shahada da tsarkakewa. 2. Jagoranci a Lokacin Karbala: A cikin sansanin Karbala: Sayyida Zainab ita ce ta rike mata da yara, tana ƙarfafa su da jimrewa. Ta kasance mai karfafa gwiwar su Ummu Kulthum, Ruqayya, Fatima Sughra, da sauran mata da yara a cikin sansani. Bayan shahadar Imam Husain (AS): A lokacin da dakarun Yazid suka kashe Imam Husain da sahabbansa, Sayyida Zainab ce ta jagoranci kula da yara...

Gudummawar Malaman Shi’a Magabata a Fannin Ƙira’o’in Alkur'ani.

Gudummawar Malaman Shi’a Magabata a Fannin Ƙira’o’in Alkur'ani. Raddi Zuwa Ga Jalo Jalingo Alhamdulillah yau dai wannan ƙasurgumin bawahabiye Nasibi ya yarda cewa: "Ƴan Sh'a sun yarda da Alkur'ani, shi yasa ya tsallaka zuwa ga cewa basu "hidimta wajen ruwaito ruwayoyin Alkur'anin ba" Wani abin dariya: Ƴan Shi'a da ake cewa basu yarda da Alkur'ani ba sai gashi yau Jalo Jalingon yana naƙalto wata magana daga littafin tafsirin ɗaya daga Manyan malaman shi'a). Don haka zamu iya gane ƙaryar Jalo Jalingo a nan ta hanya kamar haka: 1. Mahimmancin ƙira’a a Mahangar Shi’a: A mahangar Shi’a, ƙira’a (karatun lafazin Alkur’ani) wata hanya ce ta tsarkake maganar Allah da tabbatar da lafazinsa kamar yadda aka saukarwa Annabi Muhammad (S), malaman Shi’a sun bayar da gudummawa ta musamman ta hanyoyi da dama, Misali: 2. Ƙira’ar Imam Ali (a.s.): Ƙira’ar Imam Ali (a.s.), tushe ce na ƙira’o’i daban-daban. Imam Ali (a.s.) yana ɗaya daga cikin waɗanda suka haddace ...

Darasi

An rawaito daga Amirul Muminin Ali (a.s) yace: «Babu wani yini da yake wucewa ga ɗan Adam face sai wannan yini ya ce masa: 'Ni sabuwar rana ce (gareka), kuma ni shaida ne a kanka, Ka faɗi magana ta alheri kuma ka aikata alheri a cikina, zan zamo maka shaida a kan haka a ranar kiyama, kuma ba za ka sake gani na ba bayan yau.'» Barka Da Safiya. Emran Darussalam