A duk sanda zuciyarku taji tana kewar ganin Imamul-Hujjah (Atfs) to ku dubi shafukan Alkur'ani... Sheikh Muhammad Taƙi Bahja (QS). Imam al-Sadiq (as) ya ce: “Al-Qur’ani alkawarin Allah ne ga halittunsa, don haka ya kamata Musulmi ya duba cikin wannan alkawari, kuma ya karanta daga cikinsa kowace rana ayoyi hamsin (50) (alal aƙall)... Alkafi Juz'i na 2, Shafi na 609. Imam Ali (AS) Yace: “Ku koyi karatun Al-Qur’ani, domin shi ne mafi kyawun zance. Ku zurfafa ilimi a cikinsa... Ku nemi warkarwa da haskensa, domin shi ne warakar zukata, Kuma ku kyautata karanta shi, domin shi ne mafi amfanin labarai.” 📚 Nahjul Balagha, Hikima ta 110. Ya Allah Ka Bamu Ikon Karanta Littafinka A Koda Yaushe. Mon, Jul 28 2025, Emran Darussalam.
Halin Ƙunci Da Tashin Hankali Da Al-ummar Gaza Ke Ciki. Al-ummar Gaza na fuskantar wani mummunan hali na yunwa da tashin hankali, sakamakon hare-haren da HKI ke kaiwa ba kakkautawa tun watanni da suka gabata. Yara da mata da tsofaffi na mutuwa kowace rana saboda yunwa, rashin magunguna, da rushewar cibiyoyin lafiya da rashin abinci. An kulle hanyoyin shigar kayan agaji gaba ɗaya, lamarin da ya jefa al’ummar cikin mummunan hali. Duk da wannan bala’i mai tsanani, yawancin ƙasashen Larabawa na kallon abin yana faruwa ba tare da matakin taimako mai ma’ana ba. Wasu daga cikinsu ma suna toshe hanyoyin agaji, yayin da wasu ke nuna shiru tamkar ba su da alhakin addini ko na ɗan Adam. Wannan ya jefa al’umma cikin ƙunci, tare da nuna gazawar haɗin kan Larabawa da kuma ƙarancin damuwa da rayukan ‘yan’uwa musulmi a Gaza. Halin Gaza darasi ne ga duniya baki ɗaya: ko da akwai 'yan'uwa a addini da harshe, sai an sami mutanen da ke da haƙiƙanin damuwa da shiri don taimakawa, in ba ...