Skip to main content

Posts

Showing posts from May, 2023

{قُلْ لَئِنِ اجْتَمَعَتِ الْإِنْسُ وَالْجِنُّ عَلَى أَنْ يَأْتُوا بِمِثْلِ هَذَا الْقُرْآنِ لَا يَأْتُونَ بِمِثْلِهِ وَلَوْ كَانَ بَعْضُهُمْ لِبَعْضٍ ظَهِيرًا}

Wahabiyanci A Mizani Part ( 5 )

- Wahabiyawa Da Khawarijh. - Wani abin da zai baka mamaki shine: idan ka duba da kyau zaka ga yadda kamanceceniya yake tsakanin Wahabiyawa da Khawarijawa ta yadda suka karkace daga sauran al'ummar musulmi, ga kaɗan daga inda suke kama: 1 - Khawarijawa sun saɓa da dukkan musulmi inda suke cewa: "Haƙiƙa wanda ya aikata kabira kafiri ne, haka nan wahabiyawa suma sun kafirta duka musulmin da basu ba akan kabira.  Duba littafin: - كشف الشبهات لمحمد بن عبد الوهاب. - تطهير الإعتقاد للصنعاني. 2 - Khawarijawa sun fitar da hukuncin cewa: "Dukkan gidan da ake aikata kabaa'ir  ya halasta a yaƙi wannan gidan (Ai jinin su ya halasta da dukiyar su, haka Wahabiyawa suka fidda hukunci cewa a yaƙi gidan da ake aikata kabaa'ir, jini da dukiyar su ya halasta a sheƙar dashi. 3 - Wahabiyawa suna kama da Khawarijawa wajen tsanani cikin addini da daskarewa cikin fahimtar addinin, Khawarijawa a yayin da suka karanta fadin Allah cewa: (إن الحكم إلا لله) sai suka ce: wanda ya ha...

Wahabiyanci A Mizani Part ( 4 )

- Wahabiyawa da sauran musulmi (Bidi'ar wahabiyawa mai girma). - Yana daga Aƙidar wahabiyawa cewa: sunyi imani cewa: su kaɗai ne ma'abota tauhidi tsantsa, amma sauran musulmai waɗanda basu ba mushrikai ne, kuma jinin su da dukiyar su ya halasta, sannan sun halasta a yaƙe su, sannan koda sun furta kalmar nan ta (La'ilaaha illallah Muhammad rasulullah) bata wadatarwa, muddin dai sunyi imani da tabarruki da ƙabarin manzon Allah (S) - suna nufin ziyarar sa da neman ceton sa - shi yasa suke cewa: duk musulmin da yayi imani da ziyaran ƙabari koda na manzon Allah Muhammad (S) ne mushriki ne, kuma shirkan sa tafi na mutanen jahiliyya masu bautan gumaka tsanani. Zaku samu wannan i'itiƙadi nasu a manyan-manyan litattafan su kamar: - الرسائل العملية التسع لمحمد بن عبد الوهاب : 79. - تطهير الإعتقاد للصنعاني : 7، 12 ، 35. - فتح المجيد : 40 - 41. - ورسالة أربع القواعد. -  ورسالة كشف الشبهات لمحمد بن عبد الوهاب ، وغيرها ). - Haka nan idan ka duba shi wannan littafi na كشف ...

Wahabiyanci A Mizani Part ( 3 ).

Tushen fikirar wahabiyanci: -  Wahabiyya sun kasa Aƙida zuwa kaso biyu: ✓- Na farko: Aƙida wanda yazo daga nassi (Kitabu wassunnah)...Suna ikirarin cewa suna ɗauko shi ne kai tsaye daga kitabu wassunnah (Abin nufi Qur'ani da hadith) ba tare da komawa ijitihadi da Mujitahidai ba, sawa'un waɗan nan Mujitahidai daga sahabbai ne ko tabi'ai ko wasun su daga malaman da suka kaiga marhalan ijitihadi. ✓- Na biyu: Aƙida wanda baizo a nassi ba, sunyi ikirarin cewa: a duk sanda basu samu nassi akan wani abu ba suna komawa ne ga fiƙihun Imam Ahmad bin Hambal da litattafan ibn Taimiyya,  amma a haƙiƙanin gaskiya idan muka duba zamu ga akwai tanaƙud cikin raba Aƙidar nan da sukayi zuwa kaso biyu, kuma zamu ga yadda ake samun karo da juna a cikin Aƙidar su, bari mu bada misali kamar haka: 1 - Idan muka duba zamu ga sun daskare akan ma'anar da suka fahimta daga zahirin wasu nassosi, kuma sun saɓawa ƙa'idar usul da ijma'i, don hakane ma Sheikh Muhammad Abdu ya sifant...

Wahabiyanci A Mizani Part ( 2 ).

Usul na fikirar wahabiyya: - Fikirar wahabiyya tana da usul guda biyu, bayyananne da ɓoyayye. - Usulin fikirar wahabiyya bayyananne shine: ikhlasi ga tauhidi (Kaɗaitakar Allah), da yaƙar shirka da gumaka. (Amma a nan gaba zamu tabbatar muku cewa babu wannan a tafiyar ta kusa kota nesa). - Usulin fikirar wahabiyya ɓoyayye shine: ƙoƙarin keta musulunci da yaɗa fitina da haddasa yaƙi tsakanin musulmi, wannan kam mun ganshi tun farkon assasa wahabiyya zuwa yau... Ta haka muka gane wannan shine asalin fikira da hadafin wahabiyya, an ƙirƙiri wancan na farkon ne domin kauda hankalin masu ƙarancin tunani, abune bayyananne cewa: wannan shi'aar na  ( إخلاص التوحيد ومحاربة الشرك) Shi'ar ne mai jawo hankali da mamaye zuciya, wanda za'a samu jawo hankalin mabiya dayawa kai harda mukhlisai, wanda basu san cewa an sanya wannan Usul na farkon ne domin bayyana na biyu ba, yazo a tarihin wahabiyya cewa: wannan da'awa an tsarata ne tare da assasa ta a asali da umurni kai tsaye daga  وزارة...

Kaɗan daga tarihin Babban Malamin Shi'a Ayatullah Sheikh Ja'afar Subhani (DZ)

Sheikh Ja'afar Subhani yana daga manya-manyan faƙihai na wannan zamanin, an haife shi a shekarar 1929 miladiyya, shekarar shi 93 a yanzu.  Shi faƙihi ne kuma Malamin usul, kuma mai tafsiri malamin tarihi, kuma malamin Aƙida, kuma failasuf. Ya fara halartan darasin Marji'in addini Sayyid Hussein burujurdi na fiƙihu da usul tun yana ƙarami, haka nan yana halartan darasin sayyid Muhammad Hujja da Sayyid Ruhullah musawi Khomeini (QS) a hauza ilimiyya a garin Qom, haka nan yayi karatu mai zurfi a wajen Sayyid Muhammad Tabataba'i. Yadda Manyan malamai suka ce: "Babu wani fage na ilimi face saida ya kutsa cikin sa, yana daga manya-manyan Malaman Shi'a na wannan zamani. Ya wallafa litattafai dayawa, har zuwa yau yana raye, Allah ya yarda dashi, ya kare shi, ya kuma yawaita masa shekarun sa. Jaridar Ahlulbaiti Online

MUTANE BASU SAN GIRMAN WANNAN MAI GIRMA BA.

Daga Imrana Haruna Darussalam  An naƙalto daga Sayyid Ahmad Khomeini (QS) yace: "Jirgin data ɗauko Imam Khomeini (QS) daga faransa zuwa Tehran a lokacin faɗuwan mulkin Sarki Shah, Imam daya sauƙa daga jirgi miliyoyin mutane ne suka tarbe shi, sun taho daga sassa daban-daban suna kiran sunan shi suna murna. A wannan lokacin ne na waiga naga fuskar Imam (QS), sai naga idanun shi suna zubda ƙwalla, Saina tambaye shi ko meya sashi kuka? bayan wannan lokaci lokacin murna ne da nasara! Sai ya amsa da cewa: "Ina kuka ne wa Imam Ali (AS)" Da ya sami irin wannan jama'a a wancan lokaci da ya canza duniya... ~ Ta nan zaka gane zaluncin da aka yiwa Imam Ali (AS). 21/05/2022 © E m r a n   D a r u s s a l a m.

Wahabiyanci A Mizani Part ( 1 ).

Wahabiyanci da wanda ya assasashi: - Ana nasabta firƙan wahabiyya ne ga Muhammad bin Abdulwahab Bn Sulaiman Annajdi, wanda aka haifa a shekarar 1115 Hijiriyya, ya rasu a shekarar 1206 Hijiriyya. Yayi karatun addini daidai gwargwado, kamar yadda a bayyane yake ya kasance mai yawan bibiya da muɗala'an labaran da suka shafi Musailama al-kazzab, da Sajah, da Aswadul Anasi, da Ɗulaiha Al-asadi, wanda tsatstsauran ra'ayin shi ya fara bayyana tun lokacin da yake karatu, mahaifin sa da wasu daga malaman sa su suka fara yaƙar wannan ra'ayi nashi, suka nuna a nisance shi, inda suke cewa: "Wannan zai ɓata, kuma zai ɓatar da dukkan waɗanda suka nisanci Allah kuma suka kasance shaƙiyyai". A shekarar 1143 Hijiriyya ya bayyana da'awar sa zuwa ga sabuwar mazhabin sa, amma mahaifin sa da wasu daga malaman sa suka yi ƙoƙarin tsaida shi tare da tunkarar sa, suka karya karsashin kiran nasa, har zuwa lokacin da mahaifinsa ya rasu a shekarar 1153 Hijiriyya, a nanne ya s...

DAGA YAU TSARIN LARABA 17-5-2023. LAMBOBIN BAI-ƊAYA NA HUKUMAR SADARWA TA ƘASA ZA SU FARA AIKI A NAJERIYA.

Lambobin Da Ake Amfani Da Su Domin Saka Kuɗi, Duba Kuɗi Da Sauran Su Na Kamfanonin Sadarwa irin su MTN, AIRTEL, GLO, 9MOBILE Da Sauransu Zasu Daina Aiki Daga Yau Laraba 17/05/2023 Domin Bin Sabon Tsarin Hukumar Sadarwa Ta Ƙasa Wato NCC.  Daga Yanzu Zaku iya Duba Waɗannan Abubuwan Daga Ƙasa Akowanne Irin Layi Kuke Da Shi.  Call Center 300 Rancen Kudi ko Data *303# Tsayar da kowane irin Tsari da ka shiga *305# Duba Account Balance (Asusu) *310# Sa Airtime (Kati) *311*Num# Siyan Data'r Kamfani *312#  Tura Kuɗi Ko Tura Data *321#  Duba Data Balance *323# NIN Link 996 Do Not Disturb (DND) 2442. Wannan Sabbin Tsarin Sunayi A Kowanne Layi Idan Kana Aiki Dashi A Najeriya ✅ A Tura Zuwa ga  Al'umma Saboda Suma Su Ƙaru

Wannan Shine Ɗan Ja'afariyya!

Ruwaya daga Imam Sadik (AS) yace: "Haƙiƙa mutumin da ya kasance daga cikin ku mai tsantseni a cikin addinin sa, yayi gaskiya a cikin zancen sa, ya kasance mai ruƙon amana, ya kyautata ɗabi'un a cikin mutane, har ta kaiga ance wannan Ja'afari ne, wannan yana faranta min rai, kuma yana shigar min da farin ciki... Masdar: Alkafi Juz'i Na 2 Shafi Na 637.

Misali Mai Cike Da Darasi

Fitilar Ƙarshe... Sayyid Ku'i (QS) a wani muhadarar sa cikin darasi a hauza yake cewa: "misali akwai wani birni da mutanen wannan birni ke rayuwa cikin duhu da hargitsi da karo da juna sabo da tsananin duhu, amma kuma sarkin wannan gari mutum ne mai hikima, a binciken sa sai ya gano wata fitila da zata haskaka duka birnin, sai ya kawo wannan fitila ya sanya shi domin mutane su amfana da hasken sa, kowa yayi farin ciki (kan samun wannan fitila), amma bayan wasu ƴan kwanaki sai aka samu wasu suka jefi fitilar suka fasa shi, da yake sarkin garin mutum ne mai son al'ummar sa sai ya kawo wani fitilan daban ya sanya, suka ƙara fasa shi, ya ƙara sanyawa suka fasa, harta kaiga ya sanya fitilu goma sha ɗaya, amma suna fasawa, fitila ɗaya ce ta rage a gurin shi, Shin ya ya kamata yayi? Idan ya fito da ragowar wannan fitila mutanen gari zasu ƙara fasa shi su rayu (su) da zuriyar su cikin duhu. Menene matsayar hikima da hankali a nan? Hikima da hankali suna cewa: "Ras...

Darasin yau