Skip to main content

Posts

Showing posts from April, 2023

Albishir Ga Ƴan Shi'ar Ali (AS)

An ruwaito daga Imam Ali (AS) yace: "Wanda ya nufe mu to yayi ruƙo da maganar mu, yayi aiki da aikin mu, domin mu Ahlul-baiti muna da ceto kuyi gwagwarmaya domin haɗuwa damu a tafki (alkausar), domin mu zamu tsayar da maƙiyan mu, mu shayar da mabiyan mu, wanda yasha bazai ƙara jin ƙishirwa ba" Bihar Al'anwar

Daruusan Rayuwa na 2.

Ɗaya daga darussa masu muhimmanci a rayuwa shine: "Ya kamata mutum yayi ƙoƙari ya zama karbabbe a gurin Allah, kuma ya yi iya ƙoƙarin sa ba tare da ya damu da ra’ayin mutane game da shi ba". Sayyid Hadi Mudarrisi (DZ)

"اللَّهُمَّ لا تَجْعَلُهُ آخِرَ العَهْدِ مِن صِيامِي لِشَهْرِ رَمَضانَ، وَأَعُوذُ بِكَ أَنْ يَطْلُعَ فَجْرُ هذِهِ اللّيْلَةِ إِلاّ وَقَدْ غَفَرْتَ لِي"

Gareku Zainabawa 🧕

Sallar Dare.

Sallah

ZAI FANSHE KA DAGA ABUBUWAN TSORON DAKE CIKIN RAYUWAR BARZAKH.

ZAI FANSHE KA DAGA ABUBUWAN TSORON DAKE CIKIN RAYUWAR BARZAKH. An hakaito cewa "Wani Malami daga cikin ٓٓArifai yake cewa: "Na kasance ina da Maqoci sai wannan maqoci nawa ya koma ga ubangijin sa, Bayan wasu kwanaki da wafatin sa kwatsam sai na ganshi a mafarki na,Saina tambaye shi cewa ya ka samu kanka a can (Rayuwar barzakh)? Sai yace dani: ya sayyadi wlh naga Musiba da manya manyan abin tsoro, Masamman lokacin da Mala'iku guda biyu (munkar da nakir) suka zomin, Suka fara min tambayoyi masu yawa, amma ni ban iya amsa musu tambayoyin da suke min ba, sbd na rasa ikon yin magana a daidai wannan lokacin (Harshena ya kasa motsawa na zama kamar kurma)  Sai nace a raina: Niko na shiga uku, wannan wane irin axaba ne mai girma? Shin ban kasance Mu'umini a rayuwata ba? Ko ban mutu ina musulmi ba? Mala'ikun nan suka tsananta akaina da tambayoyi kuma ni na kasa basu amsa, a daidai wannan lokaci kwatsam saiga wani kyakykyawan saurayi ya bayyana, Mai sanye da kans...

A Imanin mu (Mu 'yan shi'a) cewa: Allah mai hikima ne

A Imanin mu (Mu 'yan shi'a) cewa: Allah mai hikima ne, wannan yasa tun farkon duniya da ya ajiye mutum sai ya sanya kalifan shi a doron kasa, kalifanci shi kuma shine Adam, haka bayan Adam akwai wasiyyin shi Shisu har aka isa kan annabi Nuh haka har zuwa kan manzon Allah ba'ayi wani zamani da babu kalifan Allah a doron kasa ba; har muka iso zuwa wafatin manzo (S) manzo kuma ya kasance tun yana raye baya aiken mutane biyu face sai ya sanya mutum daya a cikin su ya zamo shugaba a tsakanin su, shin kunaga wanda yake yin haka zai bar duniya ba tare da ya sanya mai ci gaba da kula da mutane a bayan shi ba? Sai ya sanya Ali a matsayin wasiyyin shi da umurnin Allah, haka har zuwa kalifofi goma sha biyu a bayan shi har zuwa kan Imam Mahdi (atfs). Kuma Allah cikin hikimar shi bazai bar qasa haka babu kalifan shi a doron ta ba, sai ya sanya na karshen su wato Imam Mahdi yayi dogon zamani, wanda har yanxu yana raye. *ABIN DUBAWA* Idan ya zama a doron kasa babu hujjar Allah...

Wasiƙun Watan Ramadan Day 26.

Day 26. An ruwaito daga Imam Hussain (AS) yace: "Wanda ya bautama Allah haƙiƙanin bauta, Allah zai bashi fiye da yadda yake zato"

Imam Khumaini Game Da Rawani.

Imam Khomeini (QS) yace: "Kada kuce wannan mai rawanin 'barawo ne, abinda ya kamata kuce shine: wannan 'barawon ya sanya rawani" a cikin fadin hakan akwai dalili bayyananne akan cewa shi rawani shi kadai ba zai yuwu a tuhume shi ba, amma qima da mutunci duka yana wajen Malamai, wanda aka yabe su a ruwayoyi dayawa, har yazo a ruwaya cewa: hatta kifaye a cikin ruwa suna nema musu gafara, Matsalar itace: wasu masu neman sai su lissafa kan su a cikin malamai da rawani bayan basu da ilimin. ~ Ya Allah ka kare Malaman mu Rabbaniyyin, ka hanemu cusa kan mu cikin Malamai. 17 APRIL 2020 EMRAN DARUSSALAM imrandarussalam99@gmail.com

Jirgin Tsira! Meka Sani Game Da Jirgin Tsira!

Jirgin Tsira! Meka Sani Game Da Jirgin Tsira! Allah maɗaukakin sarki yana cewa: وَقَالَ ارْكَبُوا فِيهَا بِسْمِ اللَّهِ مَجْرَاهَا وَمُرْسَاهَا ۚ إِنَّ رَبِّي لَغَفُورٌ رَّحِيمٌ Me Tafsirul-Amsal yace: Tsira daga ɗufana baya taɓa yiwuwa ba tare da jirgin tsira (Safinat-Annajati) ba, ba sharaɗi bane sai wannan jirgi ya zamto na katako ko ƙarfe ba, amma me yafi kyau ace wannan jirgi ya zamto addini dake kula da ɗabi'u, kuma ya bada rayuwa Kyakykyawan rayuwa,  kuma yayi juriya tare da tsayawa ƙyam a yayin da ruwan ɗufanan karkacewan fikira ya rinƙa tashi sama yana dawowa ƙasa, daga ƙarshe ya isar da mabiyan sa zuwa bakin tafki na Safinat-Annajati. A bisa wannan ne aka samu ruwayoyi dayawa daga Annabi (S) a littafin shi'a da sunnah dake nuna Ahlul-baitin sa - Imaman shiriya - masu kare addini - cewa sune (Safinatun najati) jirgin tsira nan. Abu Zaar ya kasance jingine da ɗakin ka'aba yake cewa: "Nine Abuzarr Algiffari, wanda bai sanni ba nine jundub sahabin man...

Nasiha 1

"Wanda ke sama shine a cikin zukata, Shi ɗin samamme ne a kowane guri da muhalli, Shi yafi kusa da kai, fiye da jijiyar wuyan ka, Ya kasance kusa da kai kaima ka kasance kusa dashi! shi yafi alkairi gareka akan ka kasance tare da sauran halittu, Domin shi ake nufi da buƙata, wanda bai haifa ba ba'a haife shi ba, babu ɗaya da ya kasance tamka a gareshi" ©26/04/2023. Emran Darussalam.

Nasiha 2.

"Wanda ke sama shine a cikin zukata, Shi ɗin samamme ne a kowane guri da muhalli, Shi yafi kusa da kai, fiye da jijiyar wuyan ka, Ya kasance kusa da kai kaima ka kasance kusa dashi! shi yafi alkairi gareka akan ka kasance tare da sauran halittu, Domin shi ake nufi da buƙata, wanda bai haifa ba ba'a haife shi ba, babu ɗaya da ya kasance tamka a gareshi" ©26/04/2023. Emran Darussalam.

Falalan Salatin Annabi A Daren Juma'a Da Ranar Ta.

Falalan Salatin Annabi A Daren Juma'a Da Ranar Ta. Daga Annabi (S) yace: "ku yawaita salati gareni a kowane daren juma'a, wanda daga cikin ku yafi yawaita salati gareni shi zaifi kowa kusanci dani, wanda yayi mini salati ɗari a ranar juma'a zaizo ranar ƙiyama fuskar sa tana haske, wanda kuma yayi min salati dubu a ranar juma'a bazai mutu ba har sai yaga wajen zaman shi a cikin aljanna" Masdar: Mustadrak Alwasa'el Juz'i 6. Allahumma salli ala Muhammad wa Ãli Muhammad. ©27/04/2023. Emran Darussalam.

Darrusan Rayuwa

Ɗaya daga darussa masu muhimmanci a rayuwa shine: "Ya kamata mutum yayi ƙoƙari ya zama karbabbe a gurin Allah, kuma ya yi iya ƙoƙarin sa ba tare da ya damu da ra’ayin mutane game da shi ba". Sayyid Hadi Mudarrisi (DZ)

TAWASSUL DA ƳAR MANZON ALLAH (S).

TAWASSUL DA ƳAR MANZON ALLAH (S). "Sababin dacewa ta akan rubuta littafin Mafatih Al-jinan ya samu ne don albarkan Sunan Sayyida Fadima Azzahra (AS) mai tsarki. Sheikh Qommi. Idan naji ƙunci nakan ɗauki sallaya na ne in hau saman gida sai inyi tawassul da Sayyida Fatima zahra (AS), sai komai ya daidaita. ~ Sayyid Ali Sistani. Kada ku gafala da muƙamin Sayyida Fatima zahra (AS) mai girma a cikin nafilolin ku na dare. Sheikh Ãbaadi. Ina tara dukkanin bukatu na, na tsawon shekara sai in roki Allah a Ayyamul-Fadimiyya, domin ina da yaƙinin Allah zai amsa mini. ~ Sayyid Ali Khamne'i. Da Sayyida Fatima zahra (AS) Allah yake yin afuwan munanan ayyuka. ~ Sheikh Wahid Alkurasani. 08 November 2022. © Emran Darussalam.

GIRMAMAWAN MUSULUNCI GA MACE.

- Addinin musulunci ya tausayawa Mace yayin da ya sauƙe ciyarwan  ƴayan ta da mijin ta da iyayen ta daga kanta, hatta ciyar da kanta bai daura mata ba, ya wajabtawa iyayen ta ne a yayin da take tare dasu, ya ɗaurawa mijin ta a yayin da tayi aure. - Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya wajibcin bata cikakken sadaki, bai wajabta mata bada ko sisi ga miji ba. - Ya tausayawa mace a yayin da yace wa ɗa, "Mahaifiyar ka! Mahaifiyar ka!! Mahaifiyar ka!!! Sannan mahaifin ka", duka don girmamawa gare ta. - Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sauƙe mata farillan hajji muddin bata tare da mijin ta ko wani muharrami da zai tsare ta har zuwa dawowan ta. - Musulunci ya tausayawa mace a yayin da ya sanya bata gadon mijin ta, dana ƴan uwan ta, dana ƴayan ta, da na iyayen ta, duk kuwa da cewa babu nauyin ciyarwan kowa a kanta. - Musulunci ya tausayawa mace tare da girmamawa gareta a yayin da ya haramta ingancin auren ta babu waliyyi da shaidu, duka saboda kada a za...

HASKEN MA'ABOCIN ZAMANI (ATFS).

Sheikh Nazaar (H) yace: "Malamin mu kuma Marji'in addini Sheikh Wahid Alkurasani (DZ) yana da wani kalma da yake faɗa akan wannan sha'ani, yana yawan cewa: "Mutumin da ke so rana ta haska shi, wajibi ne a gare shi ya fita daga tsakanin gini da ƙarƙashin baranda (wato ya kasance a wajen gida), amma wanda ya kasance yana cikin gida tsakanin gini da ƙarƙashin baranda bazai taɓa yuwuawa hasken rana ya isa gare shi ba" Tofa haka nan ludufin Imam Mahdi (Atfs) game da haduwa dashi yake, domin shine hasken wannan duniya, wanda hasken shi ke haskaka zukata, wanda ke son hasken Imam ya haskaka shi wajibi ne sai ya bar tsakanin ginin hijabi da zunubi, a yayin nan ne hasken zai isa gare shi. ✓ Ya Allah ka haskaka zukatan mu da hasken Imam Mahdi (Atfs). اللهم عجل لوليك الفرج  28 October 2022. © E m r a n   D a r u s s a l a m.

Rayuwar Duniya

Ita rayuwar duniya kamar wata ayari ce dake ɗaukan matafiya zuwa gidan lahira. Kada ku ɗamfarar da zukatan ku da waɗan nan sa'oi kaɗan ɗin na wannan tafiya mai wucewa, Ba komai bace (rayuwar duniyan) illa dare wanda yanzu ne duhun zai gushe, hasken safiyan lahira ya bayyana, Ya ishe ku yin hakuri kaɗan domin gushewan wannan duhu, sai hasken lahira ya bayyana, sai ma'abota ayarin nan na duniya su isa lahira daya bayan daya. Babban Ārifi Sheikh Muhammad Taqi Misbah Yazdi (QS). 12 November 2022. © Emran Darussalam.

AQIDAR SHI'A IMAMIYYA ITHA ASHARIYYA.

Aqeedar Shi'a Imamiyya ta ginu ne akan wadannan abubuwa: IMANIN MU DA ALLAH. ● Munyi Imani cewa: Sanin Allah (S) wajibi ne akan dukkan Mukallaf da dalilin cewa Allah shike ni'imtawa. ● Allah (S) Samamme ne, ya halacci duniya da dukkan abinda ke cikin ta, haka duk wani abu da ya samu Allah ne ya samar dashi. ● Allah (S) shi ya samar da komai (Baya da buqatar wani ya samar dashi tun farko, kuma bazai kasance babu shi ba anan gaba) ● Allah (S) mai iko ne akan komai, kuma masani ne akan abinda ke fili da abinda ke 'boye. ● Allah (S) mai magana ne (Amma ba magana irin na halittu ba) da dalilin cewa: و كلم الله موسى تكليما ● Allah (S) shi kadai yake bashi da abokin tarayya, hada shi da wani shirka ne. ● Allah (S) ba murakkab bane (Wanda yake a rarrabe) sbd idan da murakkab ne da kenan zai zama yana da buqatan sauran jikin shi, kuma Allah ba mabuqaci bane. ● Allah ba jiki bane, da jiki ne da zai zama akwai buqatar wanda ya halicce shi kenan, kuma Allah shi ya samar da kanshi. ● Ba...